< اعداد 9 >

در ماه اول سال دوم پس از بیرون آمدن قوم اسرائیل از سرزمین مصر وقتی که موسی و قوم اسرائیل در صحرای سینا بودند، خداوند به موسی گفت: 1
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
«به بنی‌اسرائیل بگو که مراسم پِسَح را در موعدش به جا آورند. 2
“Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
در غروب روز چهاردهم همین ماه آن را به جا آورند. در اجرای این مراسم باید از تمام فرایض و قوانینی که من در این مورد داده‌ام پیروی کنند.» 3
A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
پس موسی به بنی‌اسرائیل گفت که مراسم عید پِسَح را به جا آورند. 4
Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
آنان عصر روز چهاردهم ماه اول، در صحرای سینا مراسم را آغاز کردند. بنی‌اسرائیل مطابق هر آنچه خداوند به موسی فرمان داده بود، عمل کردند. 5
suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
ولی عده‌ای از مردان در آن روز نتوانستند در مراسم پِسَح شرکت کنند، زیرا در اثر تماس با جنازه نجس شده بودند. ایشان نزد موسی و هارون آمده، مشکل خود را با آنان در میان گذاشتند 6
Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
و به موسی گفتند: «ما با دست زدن به بدن مرده نجس شده‌ایم. اما چرا ما نباید مثل سایر اسرائیلی‌ها در این عید به خداوند قربانی تقدیم کنیم؟» 7
suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
موسی جواب داد: «صبر کنید تا در این باره از خداوند کسب تکلیف کنم.» 8
Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
جواب خداوند از این قرار بود: 9
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
«اگر فردی از افراد بنی‌اسرائیل، چه در حال حاضر و چه در نسلهای بعد، به هنگام عید پِسَح به سبب تماس با جنازه نجس شود، یا اینکه در سفر بوده، نتواند در مراسم عید حضور یابد، باز می‌تواند عید پِسَح را برای خداوند به جا آورد، 10
“Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
ولی بعد از یک ماه، یعنی غروب روز چهاردهم از ماه دوم؛ در آن هنگام می‌تواند برهٔ پِسَح را با نان فطیر و سبزیجات تلخ بخورد. 11
Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
نباید چیزی از آن را تا صبح روز بعد باقی بگذارد و نباید استخوانی از آن را بشکند. او باید کلیه دستورهای مربوط به عید پِسَح را اجرا نماید. 12
Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
«ولی فردی که نجس نبوده و در سفر نیز نباشد و با وجود این از انجام مراسم عید پِسَح در موعد مقرر سر باز زند، باید به علّت خودداری از تقدیم قربانی به خداوند در وقت مقرر، از میان قوم اسرائیل رانده شود. او مسئول گناه خویش خواهد بود. 13
Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
اگر بیگانه‌ای در میان شما ساکن است و می‌خواهد مراسم عید پِسَح را برای خداوند به جا آورد، باید از تمامی این فرایض و قوانین پیروی نماید. این قانون برای همه است.» 14
“‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
در آن روزی که خیمهٔ عبادت بر پا شد، ابری ظاهر شده، خیمه را پوشانید و هنگام شب، آن ابر به شکل آتش درآمد و تا صبح به همان صورت باقی ماند. 15
A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
این ابر همیشه خیمه را می‌پوشانید و در شب به شکل آتش در می‌آمد. 16
Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
وقتی که ابر حرکت می‌کرد، قوم اسرائیل کوچ می‌کردند و هر وقت ابر می‌ایستاد، آنها نیز توقف می‌کردند و در آنجا اردو می‌زدند. 17
Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
به این ترتیب، ایشان به دستور خداوند کوچ نموده، در هر جایی که ایشان را راهنمایی می‌کرد، توقف می‌کردند و تا زمانی که ابر ساکن بود در همان مکان می‌ماندند. 18
Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
اگر ابر مدت زیادی می‌ایستاد، آنها هم از دستور خداوند اطاعت کرده، به همان اندازه توقف می‌کردند. 19
Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
ولی اگر ابر فقط چند روزی می‌ایستاد، آنگاه ایشان هم طبق دستور خداوند فقط چند روز می‌ماندند. 20
Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
گاهی ابر آتشین فقط شب می‌ایستاد و صبح روز بعد حرکت می‌کرد؛ ولی، چه شب و چه روز، وقتی که حرکت می‌کرد، قوم اسرائیل نیز به دنبال آن راه می‌افتادند. 21
Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
اگر ابر دو روز، یک ماه، یا یک سال بالای خیمهٔ عبادت می‌ایستاد، بنی‌اسرائیل هم به همان اندازه توقف می‌کردند، ولی به مجردی که به حرکت در می‌آمد قوم هم کوچ می‌کردند، 22
Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
به این ترتیب بود که بنی‌اسرائیل به فرمان خداوند کوچ می‌کردند و اردو می‌زدند. آنها هر آنچه را که خداوند به موسی امر می‌کرد، بجا می‌آوردند. 23
Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.

< اعداد 9 >