< اعداد 33 >
این است سفرنامهٔ قوم اسرائیل از روزی که به رهبری موسی و هارون از مصر بیرون آمدند. | 1 |
Ga wuraren da Isra’ilawa suka yi sansani sa’ad da suka fito runduna-runduna a ƙarƙashin Musa da Haruna daga Masar.
موسی طبق دستور خداوند مراحل سفر آنها را نوشته بود. | 2 |
Bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya rubuta wuraren tafiye-tafiyensu da sansaninsu. Ga yadda tafiye-tafiyen suka kasance.
آنها در روز پانزدهم از ماه اول، یعنی یک روز بعد از پِسَح از شهر رَمِسیس مصر خارج شدند. در حالی که مصریها همۀ نخستزادگان خود را که خداوند شب قبل آنها را کشته بود دفن میکردند، قوم اسرائیل با سربلندی از مصر بیرون آمدند. این امر نشان داد که خداوند از تمامی خدایان مصر قویتر است. | 3 |
Isra’ilawa sun tashi daga Rameses a rana ta goma sha biyar, ga watan fari, kashegarin Bikin Ƙetarewa. Suka fita gabagadi a gaban dukan Masarawa,
waɗanda suke binne gawawwakin’ya’yan farinsu da Ubangiji ya karkashe; gama Ubangiji ya hukunta allolinsu.
پس از حرکت از رَمِسیس، قوم اسرائیل در سوکوت اردو زدند و از آنجا به ایتام که در حاشیهٔ بیابان است رفتند. | 5 |
Isra’ilawa suka tashi daga Rameses, suka yi sansani a Sukkot.
Suka tashi daga Sukkot, suka yi sansani a Etam, a gefen hamada.
بعد به فیهاحیروت نزدیک بعل صفون رفته، در دامنهٔ کوه مجدل اردو زدند. | 7 |
Suka tashi daga Etam, suka koma baya zuwa Fi Hahirot, wajen gabashin Ba’al-Zafon, suka yi sansani kusa da Migdol.
سپس از آنجا کوچ کرده، از میان دریای سرخ گذشتند و به بیابان ایتام رسیدند. سه روز هم در بیابان ایتام پیش رفتند تا به ماره رسیدند و در آنجا اردو زدند. | 8 |
Suka tashi daga Fi Hahirot, suka ratsa cikin teku zuwa hamada, bayan sun yi tafiya kwana uku a cikin Hamadan Etam, sai suka yi sansani a Mara.
از ماره کوچ کرده، به ایلیم آمدند که در آنجا دوازده چشمهٔ آب و هفتاد درخت خرما بود، و مدتی در آنجا ماندند. | 9 |
Suka tashi daga Mara, suka tafi Elim, inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu, da itatuwan dabino guda saba’in, suka yi sansani a can.
از ایلیم به کنار دریای سرخ کوچ نموده، اردو زدند؛ | 10 |
Suka tashi daga Elim, suka yi sansani kusa da Jan Teku.
پس از آن به صحرای سین رفتند. | 11 |
Suka tashi daga Jan Teku, suka yi sansani a Hamadan Sin.
سپس به ترتیب به دُفقه، | 12 |
Suka tashi daga Hamadan Sin, suka yi sansani a Dofka.
Suka tashi daga Dofka, suka yi sansani a Alush.
و رفیدیم که در آنجا آب نوشیدنی یافت نمیشد، رفتند. | 14 |
Suka tashi daga Alush, suka yi sansani a Refidim, inda babu ruwan da mutane za su sha.
از رفیدیم به صحرای سینا و از آنجا به قبروت هتاوه و سپس از قبروت هتاوه به حصیروت کوچ کردند و بعد به ترتیب به نقاط زیر رفتند: از حصیروت به رتمه، از رتمه به رمون فارص، از رمون فارص به لبنه، از لبنه به رسه، از رسه به قهیلاته، از قهیلاته به کوه شافر، از کوه شافر به حراده، از حراده به مقهیلوت، از مقهیلوت به تاحت، از تاحت به تارح، از تارح به متقه، از متقه به حشمونه، از حشمونه به مسیروت، از مسیروت به بنییعقان، از بنییعقان به حورالجدجاد، از حورالجدجاد به یطبات، از یطبات به عبرونه، از عبرونه به عصیون جابر، از عصیون جابر به قادش (در بیابان صین)، از قادش به کوه هور (در مرز سرزمین ادوم). | 15 |
Suka tashi daga Refidim, suka yi sansani a Hamadan Sinai.
Suka tashi daga Hamadan Sinai, suka yi sansani a Kibrot Hatta’awa.
Suka tashi daga Kibrot Hatta’awa, suka yi sansani a Hazerot.
Suka tashi daga Hazerot, suka yi sansani a Ritma.
Suka tashi daga Ritma, suka yi sansani a Rimmon Ferez.
Suka tashi daga Rimmon Ferez, suka yi sansani a Libna.
Suka tashi daga Libna, suka yi sansani a Rissa.
Suka tashi daga Rissa, suka yi sansani a Kehelata.
Suka tashi daga Kehelata, suka yi sansani a Dutsen Shefer.
Suka tashi daga Dutsen Shefer, suka yi sansani a Harada.
Suka tashi daga Harada, suka yi sansani a Makhelot.
Suka tashi daga Makhelot, suka yi sansani a Tahat.
Suka tashi daga Tahat, suka yi sansani a Tera.
Suka tashi daga Tera, suka yi sansani a Mitka.
Suka tashi daga Mitka, suka yi sansani a Hashmona.
Suka tashi daga Hashmona, suka yi sansani a Moserot.
Suka tashi daga Moserot, suka yi sansani a Bene Ya’akan.
Suka tashi daga Bene Ya’akan, suka yi sansani a Hor Haggidgad.
Suka tashi daga Hor Haggidgad, suka yi sansani a Yotbata.
Suka tashi daga Yotbata, suka yi sansani a Abrona.
Suka tashi daga Abrona, suka yi sansani a Eziyon Geber.
Suka tashi daga Eziyon Geber, suka yi sansani a Kadesh, cikin Hamadan Zin.
Suka tashi daga Kadesh, suka yi sansani a Dutsen Hor, a iyakar Edom.
وقتی در دامنهٔ کوه هور بودند، هارون کاهن به دستور خداوند به بالای کوه هور رفت. وی در سن ۱۲۳ سالگی، در روز اول از ماه پنجم سال چهلم؛ بعد از بیرون آمدن بنیاسرائیل از مصر، در آنجا وفات یافت. | 38 |
Bisa ga umarni Ubangiji, Haruna firist, ya hau Dutsen Hor, inda ya mutu a rana ta fari ga watan biyar, a shekara ta arba’in, bayan Isra’ilawa suka fito daga Masar.
Haruna yana da shekara ɗari da ashirin da uku, sa’ad da ya mutu a Dutsen Hor.
در این هنگام بود که پادشاه کنعانی سرزمین عراد (واقع در نِگِب کنعان)، اطلاع یافت که قوم اسرائیل به کشورش نزدیک میشوند. | 40 |
Sarki Arad Bakan’ane, wanda yake zaune a Negeb na Kan’ana, ya ji labari cewa Isra’ilawa suna zuwa.
پس اسرائیلیها از کوه هور به صلمونه کوچ کردند و در آنجا اردو زدند. | 41 |
Suka tashi daga Dutsen Hor, suka yi sansani a Zalmona.
Suka tashi daga Zalmona, suka yi sansani a Funon.
پس از آن به اوبوت کوچ کردند | 43 |
Suka tashi daga Funon, suka yi sansani a Obot.
و از آنجا به عییعباریم در مرز موآب رفته، در آنجا اردو زدند. | 44 |
Suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim, a iyakar Mowab.
سپس به دیبون جاد رفتند | 45 |
Suka tashi daga Iyim, suka yi sansani a Dibon Gad.
و از دیبون جاد به علمون دبلاتایم | 46 |
Suka tashi daga Dibon Gad, suka yi sansani a Almon Dibilatayim.
و از آنجا به کوهستان عباریم، نزدیک کوه نبو کوچ کردند. | 47 |
Suka tashi daga Almon Dibilatayim, suka yi sansani a duwatsun Abarim, kusa da Nebo.
سرانجام به دشت موآب رفتند که در کنار رود اردن در مقابل شهر اریحا بود. | 48 |
Suka tashi daga duwatsun Abarim, suka yi sansani a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
در دشت موآب، از بیتیشیموت تا آبل شطیم در جاهای مختلف، کنار رود اردن اردو زدند. | 49 |
A can filayen Mowab, suka yi sansani kusa da Urdun ɗaura da Bet-Yeshimot har zuwa Abel-Shittim.
زمانی که آنها در کنار رود اردن، در مقابل اریحا اردو زده بودند، خداوند به موسی فرمود که به قوم اسرائیل بگوید: «وقتی که از رود اردن عبور کردید و به سرزمین کنعان رسیدید، | 50 |
A filayen Mowab kusa da Urdun ɗaura da Yeriko ne Ubangiji ya ce wa Musa,
“Ka gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
باید تمامی ساکنان آنجا را بیرون کنید و همهٔ بتها و مجسمههایشان را از بین ببرید و عبادتگاهای واقع در بالای کوهها را که در آنجا بتهایشان را پرستش میکنند خراب کنید. | 52 |
ku kori dukan mazaunan ƙasar a gabanku. Ku rurrushe sassaƙaƙƙun duwatsu, da siffofinsu na zubi, ku kuma rurrushe dukan masujadansu na kan tudu.
من سرزمین کنعان را به شما دادهام. آن را تصرف کنید و در آن ساکن شوید. | 53 |
Ku mallaki ƙasar, ku kuma zauna a ciki, gama na ba ku ƙasar, ku mallake ta.
زمین به تناسب جمعیت قبیلههایتان به شما داده خواهد شد. قطعههای بزرگتر زمین به قید قرعه بین قبیلههای بزرگتر و قطعههای کوچکتر بین قبیلههای کوچکتر تقسیم شود. | 54 |
Ku rarraba ƙasar ta wurin jefan ƙuri’a, bisa ga kabilanku. Kabilar da take babba, a ba ta babban gādo, ƙarami kabila kuwa, a ba ta ƙaramin gādo. Duk abin da ƙuri’a ta ba su, shi zai zama nasu. Ku rarraba wannan bisa zuriyar kakanninku.
ولی اگر تمامی ساکنان آنجا را بیرون نکنید، باقیماندگان مثل خار به چشمهایتان و چون تیغ در پهلویتان فرو خواهند رفت و شما را در آن سرزمین آزار خواهند رساند. | 55 |
“‘Amma in ba ku kori mazaunan ƙasar ba, waɗanda kuka bari su ci gaba da zama, za su zama muku hakki a idanunku, da kuma ƙayayyuwa a bayanku. Za su ba ku wahala a ƙasar da kuke zama.
آری، اگر آنان را بیرون نکنید آنگاه من شما را هلاک خواهم کرد همانطور که قصد داشتم شما آنها را هلاک کنید.» | 56 |
Sa’an nan kuwa zan yi muku abin da na shirya yin musu.’”