< داوران 5 >
آنگاه دبوره و باراق این سرود را به مناسبت پیروزی خود سراییدند: | 1 |
A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
«خداوند را ستایش کنید! رهبران اسرائیل شجاعانه به جنگ رفتند، و قوم با اشتیاق از آنها پیروی نمودند. | 2 |
“Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
«ای پادشاهان و ای حکام گوش کنید! من در وصف خداوند خواهم سرایید، و برای خدای اسرائیل سرود خواهم خواند. | 3 |
“Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
«ای خداوند، وقتی از سعیر بیرون آمدی و صحرای ادوم را ترک فرمودی، زمین متزلزل گردید و آسمان قطرات بارانش را فرو ریخت. | 4 |
“Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
آری، حتی کوه سینا از حضور یهوه خدای اسرائیل به لرزه درآمد! | 5 |
Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
«در ایام شمجر و یاعیل شاهراهها متروک بودند. مسافران از کوره راههای پر پیچ و خم عبور میکردند. | 6 |
“A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
اسرائیل رو به زوال میرفت، تا اینکه دبوره برخاست تا همچون مادری از اسرائیل حمایت کند. | 7 |
Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
چون اسرائیل به دنبال خدایان تازه رفت، جنگ به دروازههای ما رسید. در میان چهل هزار مرد اسرائیلی، نه نیزهای یافت میشد و نه سپری. | 8 |
Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
قلب من مشتاق رهبران اسرائیل است که با اشتیاق تمام، خود را وقف کردند. خداوند را ستایش کنید، | 9 |
Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
ای کسانی که بر الاغهای سفید سوارید و بر فرشهای گرانبها مینشینید، و ای کسانی که پای پیاده راه میروید. | 10 |
“Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
گوش کنید! سرایندگان، گرد چاهها جمع شدهاند تا پیروزیهای عادلانۀ خداوند را بسرایند. آری، آنان میسرایند که چگونه خداوند اسرائیل را توسط روستائیان پیروز ساخت، و چگونه قوم خداوند از دروازههای دشمن گذشتند! | 11 |
da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
«”بیدار شو ای دبوره! بیدار شو و سرود بخوان. برخیز ای باراق! ای فرزند ابینوعم، برخیز و اسیرانت را به اسارت ببر!“ | 12 |
‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
«مردان امین از کوه سرازیر شدند، قوم خداوند برای جنگ نزد او آمدند. | 13 |
“Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
برخی از قبایل افرایم که ریشه در عمالیق دارند آمدند؛ بنیامین با مردانی بود که تو را پیروی میکردند. از ماخیر فرماندهان فرود آمدند، و از زبولون کسانی که عصای فرمانروایی در دست داشتند. | 14 |
Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
رهبران یساکار با دبوره و باراق، به دره هجوم بردند. اما قبیلهٔ رئوبین مردد بود. | 15 |
’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
چرا رئوبین در میان آغلها ماند؟ آیا میخواست به نوای نی شبانان گوش دهد؟ آری قبیلهٔ رئوبین مردد بود! | 16 |
Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
چرا جلعاد در آن سوی رود اردن ماند؟ چرا دان نزد کشتیهایش توقف نمود؟ چرا اشیر کنار دریا نزد بنادر خود ساکت نشست؟ | 17 |
Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
اما قبایل زبولون و نفتالی جان خود را در میدان نبرد به خطر انداختند. | 18 |
Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
«پادشاهان کنعان در تعنک نزد چشمههای مجدو جنگیدند، اما پیروزی را به چنگ نیاوردند. | 19 |
“Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
ستارگان از آسمان با سیسرا جنگیدند. | 20 |
Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
رود خروشان قیشون، دشمن را با خود برد. ای جان من با شهامت به پیش برو. | 21 |
Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
صدای پای اسبان دشمن را بشنوید! ببینید چگونه چهار نعل میتازند و دور میشوند! | 22 |
Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
فرشتهٔ خداوند میگوید:”میروز را لعنت کنید، ساکنانش را به سختی لعنت نمایید، زیرا به کمک خداوند نیامدند تا او را در جنگ با دشمنان یاری دهند.“ | 23 |
Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
«آفرین بر یاعیل، زن حابر قینی، خداوند او را برکت دهد، بیش از تمامی زنان خیمه نشین! | 24 |
“Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
سیسرا آب خواست، اما یاعیل در جامی ملوکانه به وی شیر داد! | 25 |
Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
آنگاه میخ چادر و چکش را برداشت و میخ را بر شقیقهاش کوبید و سرش را به زمین دوخت. | 26 |
Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
او نزد پاهای یاعیل افتاد و جان سپرد. | 27 |
A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
«مادر سیسرا از پنجرهٔ اتاقش چشم به راه او دوخته بود و میگفت:”چرا ارابهاش نمیآید؟ چرا صدای چرخهای ارابهاش را نمیشنوم؟“ | 28 |
“Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
«ندیمههای خردمندش با او همصدا شده گفتند: | 29 |
Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
”غنیمت فراوان به چنگ آوردهاند و برای تقسیم آن وقت لازم دارند. یک یا دو دختر نصیب هر سرباز میشود. سیسرا جامههای رنگارنگ به ارمغان خواهد آورد، شالهای قلابدوزی برای گردن ما با خود خواهد آورد.“ | 30 |
‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
«ای خداوند تمامی دشمنانت همچون سیسرا نابود گردند. اما کسانی که تو را دوست دارند مثل خورشید باشند وقتی در قوّتش طلوع میکند.» بعد از آن، به مدت چهل سال آرامش در سرزمین بنیاسرائیل برقرار گردید. | 31 |
“Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.