< داوران 2 >
روزی فرشتهٔ خداوند از جلجال به بوکیم آمده، به قوم اسرائیل گفت: «من شما را از مصر به سرزمینی که وعدهٔ آن را به اجدادتان دادم آوردم و گفتم که هرگز عهدی را که با شما بستهام نخواهم شکست، به شرطی که شما نیز با اقوامی که در سرزمین موعود هستند هم پیمان نشوید و مذبحهای آنها را خراب کنید؛ ولی شما اطاعت نکردید. | 1 |
Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
پس من نیز این قومها را از این سرزمین بیرون نمیکنم و آنها چون خار به پهلوی شما فرو خواهند رفت و خدایان ایشان چون تله شما را گرفتار خواهند کرد.» | 3 |
Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
وقتی فرشته سخنان خود را به پایان رسانید، قوم اسرائیل با صدای بلند گریستند. | 4 |
Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
آنها آن مکان را بوکیم نامیده، در آنجا برای خداوند قربانی کردند. | 5 |
sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
یوشع قوم اسرائیل را پس از ختم سخنرانی خود مرخص کرد و آنها رفتند تا زمینهایی را که به ایشان تعلق میگرفت، به تصرف خود درآورند. | 6 |
Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
یوشع خدمتگزار خداوند، در سن صد و ده سالگی درگذشت و او را در ملکش در تمنه حارس واقع در کوهستان افرایم به طرف شمال کوه جاعش به خاک سپردند. قوم اسرائیل در طول زندگانی یوشع و نیز ریشسفیدان قوم که پس از او زنده مانده بودند و شخصاً اعمال شگفتانگیز خداوند را در حق اسرائیل دیده بودند، نسبت به خداوند وفادار ماندند. | 7 |
Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
ولی سرانجام تمام مردم آن نسل مردند و نسل بعدی خداوند را فراموش کردند و هر آنچه که او برای قوم اسرائیل انجام داده بود، به یاد نیاوردند. | 10 |
Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
ایشان نسبت به خداوند گناه ورزیدند و به پرستش بتهای بعل روی آوردند. | 11 |
Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
آنها خداوند خدای پدران خود را که آنها را از مصر بیرون آورده بود ترک نموده، بتهای اقوام اطرافشان را عبادت و سجده میکردند، بنابراین خشم خداوند بر تمام اسرائیل افروخته شد، | 12 |
Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
زیرا آنها خداوند را ترک نموده، بتهای بعل و عشتاروت را عبادت کردند. | 13 |
domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
پس خداوند آنها را به دست دشمنانشان سپرد تا غارت شوند، به حدی که توان مقابله با دشمنان را نداشتند. | 14 |
Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
هرگاه قوم اسرائیل با دشمنان میجنگیدند، خداوند بر ضد اسرائیل عمل میکرد، همانطور که قبلاً در این مورد هشدار داده و قسم خورده بود. اما وقتی که قوم به این وضع فلاکتبار دچار گردیدند | 15 |
Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
خداوند رهبرانی فرستاد تا ایشان را از دست دشمنانشان برهانند. | 16 |
Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
ولی از رهبران نیز اطاعت ننمودند و با پرستش خدایان دیگر، نسبت به خداوند خیانت ورزیدند. آنها برخلاف اجدادشان عمل کردند و خیلی زود از پیروی خداوند سر باز زده، او را اطاعت ننمودند. | 17 |
Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
هر یک از رهبران در طول عمر خود، به کمک خداوند قوم اسرائیل را از دست دشمنانشان میرهانید، زیرا خداوند به سبب نالهٔ قوم خود و ظلم و ستمی که بر آنها میشد، دلش بر آنها میسوخت و تا زمانی که آن رهبر زنده بود به آنها کمک میکرد. | 18 |
Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
اما وقتی که آن رهبر میمرد، قوم به کارهای زشت خود برمیگشتند و حتی بدتر از نسل قبل رفتار میکردند. آنها باز به سوی خدایان بتپرستان روی آورده، جلوی آنها زانو میزدند و آنها را عبادت مینمودند و با سرسختی به پیروی از رسوم زشت بتپرستان ادامه میدادند. | 19 |
Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
پس خشم خداوند بر بنیاسرائیل افروخته شد و فرمود: «چون این قوم پیمانی را که با پدران ایشان بستم شکستهاند و از من اطاعت نکردهاند، | 20 |
Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
من نیز قبایلی را که هنگام فوت یوشع هنوز مغلوب نشده بودند، بیرون نخواهم کرد. | 21 |
ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
بلکه آنها را برای آزمودن قوم خود میگذارم تا ببینم آیا آنها چون پدران خود، مرا اطاعت خواهند کرد یا نه.» | 22 |
Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
پس خداوند آن قبایل را در سرزمین کنعان واگذاشت. او ایشان را توسط یوشع به کلی شکست نداده بود و بعد از مرگ یوشع نیز فوری آنها را بیرون نکرد. | 23 |
Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.