< ایوب 31 >

با چشمان خود عهد بستم که هرگز با نظر شهوت به دختری نگاه نکنم. 1
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
خدای قادر مطلق که در بالاست برای ما چه تدارک دیده است؟ 2
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
آیا مصیبت و بلا سرنوشت شریران و بدکاران نیست؟ 3
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
آیا او هر کاری را که می‌کنم و هر قدمی را که برمی‌دارم نمی‌بیند. 4
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
من هرگز دروغ نگفته و کسی را فریب نداده‌ام. 5
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
بگذار خدا خودش مرا با ترازوی عدل بسنجد و ببیند که بی‌گناهم. 6
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
اگر پایم را از راه خدا بیرون گذاشته‌ام، یا اگر دلم در طمع چیزهایی بوده که چشمانم دیده است، یا اگر دستهایم به گناه آلوده شده است، 7
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
باشد که غله‌ای که کاشته‌ام از ریشه کنده شود و یا شخص دیگری آن را درو کند. 8
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
اگر شیفتهٔ زن مرد دیگری شده، در کمین او نشسته‌ام، 9
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
باشد که همسرم را مرد دیگری تصاحب کند؛ 10
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
زیرا این کار زشت سزاوار مجازات است، 11
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
و مانند آتشی جهنمی می‌تواند تمام هستی مرا بسوزاند و از بین ببرد. 12
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
اگر نسبت به غلام یا کنیز خود بی‌انصافی می‌کردم، وقتی که از من شکایت داشتند، 13
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
چگونه می‌توانستم با خدا روبرو شوم؟ و هنگامی که در این باره از من سؤال می‌کرد، چه جوابی می‌دادم؟ 14
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
چون هم من و هم خدمتگزارانم، به دست یک خدا سرشته شده‌ایم. 15
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
هرگز از کمک کردن به فقرا کوتاهی نکرده‌ام. هرگز نگذاشته‌ام بیوه‌زنی در ناامیدی بماند، 16
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
یا یتیمی گرسنگی بکشد، بلکه خوراک خود را با آنها قسمت کرده‌ام 17
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
و تمام عمر خود را صرف نگهداری از آنها نموده‌ام. 18
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
اگر کسی را می‌دیدم که لباس ندارد و از سرما می‌لرزد، 19
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
لباسی از پشم گوسفندانم به او می‌دادم تا از سرما در امان بماند و او با تمام وجود برای من دعای خیر می‌کرد. 20
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
اگر من با استفاده از نفوذی که در دادگاه داشته‌ام حق یتیمی را پایمال نموده باشم 21
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
بازویم از کتفم بیفتد و دستم بشکند. 22
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
هرگز جرأت نمی‌کردم چنین کاری را انجام دهم، زیرا از مجازات و عظمت خدا می‌ترسیدم. 23
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
هرگز به طلا و نقره تکیه نکرده‌ام 24
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
و شادی من متکی به مال و ثروت نبوده است. 25
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
هرگز فریفتهٔ خورشید تابان و ماه درخشان نشده‌ام و آنها را از دور نبوسیده و پرستش نکرده‌ام؛ 26
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
چون اگر مرتکب چنین کارهایی شده بودم مفهومش این بود که خدای متعال را انکار کرده‌ام، و چنین گناهی بی‌سزا نمی‌ماند. 28
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
هرگز از مصیبت دشمن شادی نکرده‌ام، 29
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
هرگز آنها را نفرین نکرده‌ام و زبانم را از این گناه باز داشته‌ام. 30
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
هرگز نگذاشته‌ام خدمتگزارانم گرسنه بمانند. 31
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
هرگز نگذاشته‌ام غریبه‌ای شب را در کوچه بخوابد، بلکه در خانهٔ خود را به روی او باز گذاشته‌ام. 32
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
هرگز مانند دیگران به خاطر ترس از سرزنش مردم، سعی نکرده‌ام گناهانم را پنهان سازم و خاموش در داخل خانهٔ خود بنشینم. 33
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
ای کاش کسی پیدا می‌شد که به حرفهایم گوش بدهد! من دفاعیهٔ خود را تقدیم می‌کنم. بگذار قادر مطلق جواب مرا بدهد و اتهاماتی را که به من نسبت داده شده به من نشان دهد، 35
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
و من آنها را مانند تاجی بر سر می‌گذارم! 36
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
تمام کارهایی را که کرده‌ام برای او تعریف می‌کنم و سربلند در حضور او می‌ایستم. 37
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
اگر زمینی که در آن کشت می‌کنم مرا متهم سازد به اینکه صاحبش را کشته‌ام و آن را تصاحب کرده‌ام تا از محصولش استفاده برم، 38
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
باشد که در آن زمین به جای گندم، خار و به عوض جو، علفهای هرز بروید. پایان سخنان ایوب. 40
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< ایوب 31 >