< ارمیا 1 >
این کتاب حاوی سخنان ارمیا پسر حلقیا است. ارمیا یکی از کاهنان شهر عناتوت (واقع در سرزمین بنیامین) بود. | 1 |
Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
نخستین پیام خداوند در سال سیزدهم سلطنت یوشیا (پسر آمون)، پادشاه یهودا، بر ارمیا نازل شد. | 2 |
Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
پیامهای دیگری نیز در دورهٔ سلطنت یهویاقیم (پسر یوشیا، پادشاه یهودا) تا یازدهمین سال پادشاهی صدقیا (پسر یوشیا، پادشاه یهودا)، بر او نازل شد. در ماه پنجم همین سال بود که اورشلیم به تصرف درآمد و اهالی شهر اسیر و تبعید شدند. | 3 |
da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
خداوند به من فرمود: «پیش از آنکه در رحم مادرت شکل بگیری تو را انتخاب کردم. پیش از اینکه چشم به جهان بگشایی، تو را برگزیدم و تعیین کردم تا در میان مردم جهان پیامآور من باشی.» | 4 |
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
“Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
اما من گفتم: «خداوندا، این کار از من ساخته نیست! من جوانی بیتجربه هستم!» | 6 |
Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
خداوند فرمود: «چنین مگو! چون به هر جایی که تو را بفرستم، خواهی رفت و هر چه به تو بگویم، خواهی گفت. | 7 |
Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
از مردم نترس، زیرا من با تو هستم و از تو محافظت میکنم.» | 8 |
Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
آنگاه دست بر لبهایم گذاشت و گفت: «اینک کلام خود را در دهانت گذاشتم! | 9 |
Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
از امروز رسالت تو آغاز میشود! تو باید به قومها و حکومتها هشدار دهی و بگویی که من برخی از ایشان را ریشهکن کرده، از بین خواهم برد و برخی دیگر را پا برجا نگاه داشته، تقویت خواهم کرد.» | 10 |
Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
سپس فرمود: «ارمیا، نگاه کن! چه میبینی؟» گفتم: «شاخهای از درخت بادام!» | 11 |
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
فرمود: «چنین است! و این بدان معناست که مراقب خواهم بود تا هر آنچه گفتهام، انجام شود.» | 12 |
Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
بار دیگر خداوند از من پرسید: «حالا چه میبینی؟» جواب دادم: «یک دیگ آب جوش که از سوی شمال بر این سرزمین فرو میریزد.» | 13 |
Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
فرمود: «آری، بلایی از سوی شمال بر تمام اهالی این سرزمین نازل خواهد شد. | 14 |
Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
من سپاهیان مملکتهای شمالی را فرا خواهم خواند تا به اورشلیم آمده تخت فرمانروایی خود را کنار دروازههای شهر بر پا دارند و همهٔ حصارهای آن و سایر شهرهای یهودا را تسخیر کنند. | 15 |
Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
این است مجازات قوم من به سبب شرارتهایشان! آنها مرا ترک گفته، برای خدایان دیگر بخور میسوزانند و در برابر بتهایی که خود ساختهاند، سجده میکنند. | 16 |
Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
«حال، برخیز و آماده شو و آنچه که من میگویم به ایشان بگو. از آنها مترس و گرنه کاری میکنم که در برابر آنها آشفته و هراسان شوی! | 17 |
“Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
امروز تو را در برابر آنها همچون شهری حصاردار و ستونی آهنین و دیواری مفرغین، مقاوم میسازم تا در برابر تمام افراد این سرزمین بایستی، در برابر پادشاهان یهودا، بزرگان، کاهنان و همهٔ مردم. | 18 |
Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
آنها با تو به ستیز برخواهند خاست، اما کاری از پیش نخواهند برد، چون من، خداوند، با تو هستم و تو را رهایی خواهم داد.» | 19 |
Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.