< ارمیا 20 >
فَشحور کاهن، پسر اِمّیر، که رئیس ناظران خانهٔ خداوند بود، شنید که ارمیا چه نبوّتی کرده است. | 1 |
Da firist nan Fashhur ɗan Immer, babban ma’aikaci a cikin haikalin Ubangiji, ya ji Irmiya yana annabcin waɗannan abubuwa,
پس به دستور او ارمیای نبی را زدند و او را در کنار دروازهٔ بالایی بنیامین که نزدیک خانهٔ خداوند بود، در کنده قرار دادند. | 2 |
sai ya sa aka yi wa Irmiya dūka aka kuma sa shi a turu a Ƙofar Bisa na Benyamin a haikalin Ubangiji.
روز بعد، وقتی فشحور ارمیا را آزاد میکرد، ارمیا به او گفت: «فشحور، خداوند نام تو را عوض کرده است؛ او نام تو را”ساکن در وحشت“نهاده است. | 3 |
Kashegari, sa’ad da Fashhur ya fitar da shi daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashhur ba, amma ya ba ka suna Magor-Missabib.
خداوند تو و دوستانت را دچار هراس و وحشت خواهد ساخت. آنها را خواهی دید که با شمشیر دشمن کشته میشوند. خداوند اهالی یهودا را به پادشاه بابِل تسلیم خواهد کرد و او این قوم را به بابِل به اسارت خواهد برد و یا خواهد کشت. | 4 |
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan maishe ka abin razana ga kanka da kuma ga dukan abokanka; da idanunka za ka gan takobin abokan gāba yana kashe su. Zan miƙa Yahuda duka ga sarkin Babilon, wanda zai kwashe su zuwa Babilon ya kuma kashe su da takobi.
خداوند اجازه خواهد داد که دشمنان، اورشلیم را غارت کنند و تمام ثروت و اشیاء قیمتی شهر و جواهرات سلطنتی یهودا را به بابِل ببرند. | 5 |
Zan ba wa abokan gābansu dukan dukiyar wannan birni dukan amfaninsa, dukan abubuwa masu daraja na sarakunan Yahuda. Za su kwashe su ganima su kai su Babilon.
و تو ای فشحور، با تمام اعضای خانوادهات اسیر شده، به بابِل خواهید رفت و در همان جا خواهید مرد و دفن خواهید شد هم تو و هم تمام دوستانت که برای آنها به دروغ پیشگویی میکردی که اوضاع خوب و آرام است!» | 6 |
Kai kuma Fashhur, da dukan waɗanda suke a gidanka za ku tafi zaman bauta a Babilon. A can za ku mutu a kuma binne ku, da kai da dukan abokanka waɗanda ka yi musu annabce-annabcen ƙarya.’”
خداوندا، تو به من وعده دادی که کمکم کنی، ولی مرا فریفتهای؛ اما من مجبورم کلام تو را به ایشان اعلام نمایم، چون از من نیرومندتری! من مسخرهٔ مردم شدهام و صبح تا شب همه به من میخندند. | 7 |
Ya Ubangiji, ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu; ka fi ni ƙarfi, ka kuwa yi nasara. Na zama abin dariya dukan yini; kowa yana yi mini ba’a.
وقتی دهان باز میکنم تا چیزی بگویم، فریاد از نهادم برمیآید که: «خشونت و ویرانی!» آری، این پیامها از جانب خداوند مرا مایۀ رسوایی و تمسخر ساخته است. | 8 |
Duk sa’ad da na yi magana, nakan tā da murya ina furta hargitsi da hallaka. Haka maganar Ubangiji ta kawo mini zagi da reni dukan yini.
از طرف دیگر اگر نخواهم کلام تو را اعلام کنم و از جانب تو سخن بگویم، آنگاه کلام تو در دلم مثل آتش، شعلهور میشود که تا مغز استخوانهایم را میسوزاند و نمیتوانم آرام بگیرم. | 9 |
Amma in na ce, “Ba zan ambace shi ba ba zan ƙara yin magana da sunansa ba,” sai in ji maganarsa a cikina kamar wuta, wutar da aka kulle a ƙasusuwana. Na gaji da danne ta a cikina; tabbatacce ba zan iya ba.
از هر طرف صدای تهدید آنها را میشنوم و بدنم میلرزد. حتی دوستانم میگویند که از دست من شکایت خواهند کرد. آنها منتظرند که بیفتم، و به یکدیگر میگویند: «شاید او خودش را به دام بیندازد؛ آن وقت میتوانیم از او انتقام بگیریم.» | 10 |
Na ji mutane da yawa suna raɗa cewa, “Razana ta kowace fuska! Mu kai kararsa! Bari mu kai kararsa!” Dukan abokaina suna jira in yi tuntuɓe, suna cewa, “Mai yiwuwa a ruɗe shi; sai mu yi nasara a kansa mu ɗau fansa a kansa.”
ولی خداوند همچون یک مرد جنگی، نیرومند و توانا، در کنارم ایستاده است؛ پس دشمنانم به زمین خواهند افتاد و بر من چیره نخواهند شد. ایشان شکست خواهند خورد و این رسوایی همیشه بر آنها خواهد ماند. | 11 |
Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
ای خداوند لشکرهای آسمان که مردم را از روی عدل و انصاف میآزمایی و از دلها و افکار ایشان آگاهی، بگذار تا انتقام تو را از ایشان ببینم، چون داد خود را نزد تو آوردهام. | 12 |
Ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake gwada adali kana bincika zuciya duk da tunani, bari in ga sakayyarka a kansu, gama a gare ka na miƙa damuwata.
برای خداوند سرود شکرگزاری خواهم خواند و او را تمجید خواهم کرد، زیرا او مظلومان را از دست ظالمان رهایی میدهد. | 13 |
Ku rera ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannuwan mugaye.
نفرین بر آن روزی که به دنیا آمدم! نفرین بر آن روزی که مادرم مرا زایید! | 14 |
La’ananniya ce ranar da aka haife ni! Kada ranar da mahaifiyata ta haife ni ta zama mai albarka!
نفرین بر آن کسی که به پدرم مژده داد که او صاحب پسری شده و با این مژده او را شاد ساخت! | 15 |
La’ananne ne mutumin da ya kawo wa mahaifina labari, wanda ya sa shi ya yi murna cewa, “An haifa maka yaro, ɗa namiji!”
ای کاش مثل شهرهای قدیم که خداوند بدون ترحم زیر و رویشان کرد، او هم نابود شود و صبح تا شب از صدای جنگ در وحشت باشد، | 16 |
Bari mutumin ya zama kamar garuruwan da Ubangiji ya tumɓuke ba tausayi. Bari yă ji kuka da safe kururuwan yaƙi kuma da tsakar rana.
زیرا به هنگام تولدم مرا نکشت! ای کاش در شکم مادرم میمردم و رحم مادرم گور من میشد! | 17 |
Gama bai kashe ni a cikin ciki ba, da ma ya sa cikin mahaifiyata ya zama kabarina, cikinta ya fadada har abada.
من چرا به دنیا آمدم؟ آیا تنها برای اینکه در تمام زندگی شاهد سختی و اندوه باشم و عمر خود را در شرمساری و رسوایی به سر برم؟ | 18 |
Me ya sa na ma fito daga cikin ciki in ga wahala da baƙin ciki in kuma ƙare kwanakina da kunya?