< اشعیا 55 >

خداوند می‌فرماید: «ای همهٔ تشنگان، نزد آبها بیایید؛ ای همهٔ شما که پول ندارید، بیایید نان بخرید و بخورید! بیایید شیر و شراب را بدون پول بخرید و بنوشید! 1
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
چرا پول خود را خرج چیزی می‌کنید که خوردنی نیست؟ چرا دسترنج خود را صرف چیزی می‌کنید که سیرتان نمی‌کند؟ به من گوش دهید و از من اطاعت کنید تا بهترین خوراک را بخورید و از آن لذت ببرید. 2
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
«ای قوم من، با گوشهای باز و شنوا نزد من بیایید تا زنده بمانید. من با شما عهدی جاودانی می‌بندم و برکاتی را که به داوود پادشاه وعده داده‌ام به شما می‌دهم. 3
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
همان‌گونه که او سرزمینها را تسخیر کرد و قدرت مرا ظاهر ساخت، 4
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
شما نیز قومهای بیگانه را فراخواهید خواند و آنها آمده، مطیع شما خواهند شد. من که یهوه خدای مقدّس اسرائیل هستم این کار را برای خودم خواهم کرد و به شما عزت و افتخار خواهم بخشید.» 5
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
خداوند را مادامی که یافت می‌شود بطلبید، و مادامی که نزدیک است او را بخوانید. 6
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
ای گناهکاران، از کارها و فکرهای فاسد خود دست بکشید و به سوی خداوند بازگشت کنید، زیرا او بسیار بخشنده است و بر شما رحم خواهد کرد. 7
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
خداوند می‌فرماید: «فکرهای من فکرهای شما نیست، و راههای من هم راههای شما نیست. 8
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
به همان اندازه که آسمان بلندتر از زمین است، راههای من نیز از راههای شما و فکرهای من از فکرهای شما بلندتر و برتر است. 9
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
«کلام من مانند برف و باران است. همان‌گونه که برف و باران از آسمان می‌بارند و زمین را سیراب و بارور می‌سازند و به کشاورز بذر و به گرسنه نان می‌بخشند، 10
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
کلام من نیز هنگامی که از دهانم بیرون می‌آید بی‌ثمر نمی‌ماند، بلکه مقصود مرا عملی می‌سازد و آنچه را اراده کرده‌ام انجام می‌دهد. 11
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
«ای قوم من، شما با شادی از بابِل بیرون خواهید آمد و با آرامش آنجا را ترک خواهید گفت. کوهها و تپه‌های اطراف شما با شادی سرود خواهند خواند و درختان صحرا برای شما دست خواهند زد! 12
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
به جای خار و خس، درختان سبز و خوشبویی چون صنوبر و آس خواهند رویید. این معجزه، یادبودی جاودانی خواهد بود از آنچه من انجام داده‌ام.» 13
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”

< اشعیا 55 >