< اشعیا 40 >
خدای اسرائیل میفرماید: «تسلی دهید! قوم مرا تسلی دهید! | 1 |
Ta’aziyya, ku ta’azantu mutanena, in ji Allahnku.
اهالی اورشلیم را دلداری دهید و به آنان بگویید که روزهای سخت ایشان به سر آمده و گناهانشان بخشیده شده، زیرا من به اندازهٔ گناهانشان آنها را تنبیه کردهام.» | 2 |
Yi magana mai kwantar da rai ga Urushalima, ku kuma furta mata cewa aiki mai zafinta ya isa, cewa an fanshi zunubinta, cewa ta karɓi daga hannun Ubangiji ninki biyu saboda dukan zunubanta.
صدایی میشنوم که میگوید: «راهی از وسط بیابان برای آمدن خداوند آماده کنید. راه او را در صحرا صاف کنید. | 3 |
Muryar wani tana kira cewa, “A cikin hamada ku shirya hanya saboda Ubangiji; ku miƙe manyan hanyoyi domin Allahnmu a cikin jeji.
درهها را پر کنید؛ کوهها و تپهها را هموار سازید؛ راههای کج را راست و جادههای ناهموار را صاف کنید. | 4 |
Za a cike kowane kwari, a baje kowane dutse da kowane tudu; za a mayar da karkatattun wurare su zama sumul, munanan wurare kuma su zama da kyau.
آنگاه شکوه و جلال خداوند ظاهر خواهد شد و همهٔ مردم آن را خواهند دید. خداوند این را وعده فرموده است.» | 5 |
Za a kuma bayyana ɗaukakar Ubangiji, dukan mutane kuwa za su gan ta. Gama Ubangiji da kansa ne ya yi magana.”
بار دیگر آن صدا میگوید: «با صدای بلند بگو!» پرسیدم: «با صدای بلند چه بگویم؟» گفت: «با صدای بلند بگو که انسان مانند علف است. تمام زیبایی او همچون گل صحراست که پژمرده میشود. | 6 |
Muryar tana cewa, “Ka yi shela.” Na kuwa ce, “Me zan yi shelar?” “Dukan mutane kamar ciyawa suke, kuma dukan ɗaukakarsu kamar furannin jeji ne.
وقتی خدا میدمد علف خشک میشود و گل پژمرده. بله، انسان مانند علف از بین میرود. | 7 |
Ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, domin Ubangiji ya hura iska a kansu. Tabbatacce mutane ciyawa ne.
گیاه خشک میشود و گل پژمرده میگردد، اما کلام خدای ما برای همیشه باقی میماند.» | 8 |
Hakika ciyawa takan yanƙwane, furanni kuma su yi yaushi, amma maganar Allahnmu tana nan daram har abada.”
ای قاصد خوش خبر، از قلهٔ کوه، اورشلیم را صدا کن. پیامت را با تمام قدرت اعلام کن و نترس. به شهرهای یهودا بگو: «خدای شما میآید!» | 9 |
Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Sihiyona, ka haura a bisa dutse. Kai da ka kawo labari mai daɗi wa Urushalima, ka tā da muryarka ka yi ihu, ka ɗaga ta, kada ka ji tsoro; faɗa wa garuruwan Yahuda, “Ga Allahnku!”
بله، خداوند یهوه میآید تا با قدرت حکومت کند. پاداشش همراه او است و هر کس را مطابق اعمالش پاداش خواهد داد. | 10 |
Duba, Ubangiji Mai Iko Duka yana zuwa da iko, hannunsa kuma yana yin mulki dominsa. Duba, ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa kuma na rakiyarsa.
او مانند شبان، گلهٔ خود را خواهد چرانید؛ برهها را در آغوش خواهد گرفت و میشها را با ملایمت هدایت خواهد کرد. | 11 |
Yakan lura da garkensa kamar makiyayi. Yakan tattara tumaki wuri ɗaya yă riƙe su kurkusa da ƙirjinsa; a hankali kuma yakan bi da masu ba da mama.
آیا کسی غیر از خدا میتواند اقیانوس را در دست نگه دارد و یا آسمان را با وجب اندازه گیرد؟ آیا کسی غیر از او میتواند خاک زمین را در ترازو بریزد و یا کوهها و تپهها را با قَپّان وزن کند؟ | 12 |
Wane ne ya auna ruwaye a tafin hannunsa, ko kuwa ya gwada tsawon sammai da fāɗin tafin hannunsa? Wane ne ya riƙe ƙurar ƙasa a kwando, ko kuwa ya auna nauyin duwatsu a magwaji, tuddai kuma a ma’auni?
کیست که بتواند به روح خداوند پند دهد؟ کیست که بتواند معلم یا مشاور او باشد؟ | 13 |
Wane ne ya fahimci zuciyarUbangiji, ko kuwa ya koya masa a matsayin mashawarcinsa?
آیا او تا به حال به دیگران محتاج بوده است که به او حکمت و دانش بیاموزند و راه راست را به او یاد دهند؟ | 14 |
Wane ne Ubangiji ya nemi shawararsa don yă ganar da shi, wane ne kuma ya koya masa hanyar da ta dace? Wane ne ya koya masa sani ko ya nuna masa hanyar fahimta?
به هیچ وجه! تمام مردم جهان در برابر او مثل قطرهٔ آبی در سطل و مانند غباری در ترازو، ناچیز هستند. همهٔ جزایر دنیا برای او گردی بیش نیستند و او میتواند آنها را از جایشان تکان دهد. | 15 |
Tabbatacce al’ummai suna kama da ɗigon ruwa a cikin bokiti an ɗauke su a matsayin ƙura a kan magwaji; yakan auna tsibirai sai ka ce ƙura mai laushi.
اگر تمام حیوانات لبنان را برای خدا قربانی کنیم باز کم است و اگر تمام جنگلهای لبنان را برای روشن کردن آتش قربانی به کار بریم باز کافی نیست. | 16 |
Itatuwan Lebanon ba su isa a yi wutar bagade da su ba, balle dabbobinsa su isa yin hadayun ƙonawa.
تمام قومها در نظر او هیچ هستند و ناچیز به شمار میآیند. | 17 |
A gabansa dukan al’ummai ba kome ba ne; ya ɗauke su ba a bakin kome ba kuma banza ne kurum.
چگونه میتوان خدا را توصیف کرد؟ او را با چه چیز میتوان مقایسه نمود؟ | 18 |
To, ga wane ne za ka kwatanta Allah? Wace siffa za ka kwatanta shi da ita?
آیا میتوان او را با یک بت مقایسه کرد؟ بُتی که بت ساز آن را ساخته و با طلا پوشانده و به گردنش زنجیر نقرهای انداخته است؟ | 19 |
Gunki dai, maƙeri kan yi zubinsa, maƙerin zinariya kuma yă ƙera shi da zinariya yă kuma sarrafa masa sarƙoƙin azurfa.
فقیری که نمیتواند خدایانی از طلا و نقره درست کند، درختی مییابد که چوبش با دوام باشد و آن را به دست صنعتگری ماهر میدهد تا برایش خدایی بسازد، خدایی که حتی قادر به حرکت نیست! | 20 |
Mutumin da talauci ya sha kansa da ba zai iya miƙa irin hadayar nan ba kan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yakan nemi gwanin sassaƙa don yă sassaƙa masa gunkin da ba zai fāɗi ba.
آیا تا به حال ندانستهاید و نشنیدهاید و کسی به شما نگفته که دنیا چگونه به وجود آمده است؟ | 21 |
Ba ku sani ba? Ba ku taɓa ji ba? Ba a faɗa muku daga farko ba? Ba ku fahimta ba tun kafawar duniya?
خدا دنیا را آفریده است؛ همان خدایی که بر فراز کرهٔ زمین نشسته و مردم روی زمین در نظر او مانند مورچه هستند. او آسمانها را مثل پرده پهن میکند و از آنها خیمهای برای سکونت خود میسازد. | 22 |
Yana zaune a kursiyi a bisa iyakar duniya, kuma mutanenta suna kama da fāra. Ya miƙa sammai kamar rumfa, ya kuma shimfiɗa su kamar tentin da za a zauna a ciki.
او رهبران بزرگ دنیا را ساقط میکند و از بین میبرد. | 23 |
Yakan mai da sarakuna ba kome ba yă mai da masu mulkin wannan duniya wofi.
هنوز ریشه نزده خدا بر آنها میدمد، و آنها پژمرده شده، مثل کاه پراکنده میگردند. | 24 |
Ba da jimawa ba bayan an shuka su, ba da jimawa ba bayan an dasa su, ba da jimawa ba bayan sun yi saiwa a ƙasa, sai yă hura musu iska su yanƙwane, guguwa kuma ta kwashe su kamar yayi.
خداوند قدوس میپرسد: «شما مرا با چه کسی مقایسه میکنید؟ چه کسی میتواند با من برابری کند؟» | 25 |
“Ga wa za ku kwatanta ni? Ko kuwa wa yake daidai da ni?” In ji Mai Tsarkin nan.
به آسمانها نگاه کنید! کیست که همهٔ این ستارگان را آفریده است؟ کسی که آنها را آفریده است از آنها مثل یک لشکر سان میبیند، تعدادشان را میداند و آنها را به نام میخواند. قدرت او آنقدر عظیم است که نمیگذارد هیچکدام از آنها گم شوند. | 26 |
Ku ɗaga idanunku ku duba sammai. Wane ne ya halicce dukan waɗannan? Wane ne ya fitar da rundunar taurari ɗaya-ɗaya, yana kiransu, kowanne da sunansa. Saboda ikonsa mai girma da kuma ƙarfinsa mai girma, babu ko ɗayansu da ya ɓace.
پس، ای اسرائیل، چرا میگویی خداوند رنجهای مرا نمیبیند و با من به انصاف رفتار نمیکند؟ | 27 |
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
آیا تا به حال ندانسته و نشنیدهای که یهوه خدای سرمدی، خالق تمام دنیا هرگز درمانده و خسته نمیشود و هیچکس نمیتواند به عمق افکار او پی ببرد؟ | 28 |
Ba ku sani ba? Ba ku ji ba? Ubangiji madawwamin Allah ne, Mahaliccin iyakokin duniya. Ba zai taɓa gaji ko yă kasala ba, kuma fahimtarsa ya wuce gaban ganewar mutum.
او به خستگان نیرو میبخشد و به ضعیفان قدرت عطا میکند. | 29 |
Yakan ba da ƙarfi ga waɗanda suka gaji yă kuma ƙara ƙarfi ga marasa ƙarfi.
حتی جوانان هم درمانده و خسته میشوند و دلاوران از پای در میآیند، | 30 |
Ko matasa ma kan gaji su kuma kasala, samari kuma kan yi tuntuɓe su fāɗi;
اما آنانی که به خداوند امید بستهاند نیروی تازه مییابند و مانند عقاب پرواز میکنند؛ میدوند و خسته نمیشوند، راه میروند و ناتوان نمیگردند. | 31 |
amma waɗanda suka dogara ga Ubangiji za su sabunta ƙarfinsu. Za su yi firiya da fikafikai kamar gaggafa; za su kuma yi gudu ba kuwa za su gaji ba, za su yi tafiya ba kuwa za su kasala ba.