< اشعیا 22 >

این پیغام دربارۀ اورشلیم، وادی رویا است: چه شده است؟ چرا مردم شهر به پشت بامها می‌دوند؟ 1
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
در تمام شهر غوغا برپاست! برای این شهر شاد و پر جنب و جوش چه پیش آمده است؟ مردان اورشلیم کشته شده‌اند اما نه در جنگ، و نه با شمشیر. 2
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
همهٔ رهبران با هم فرار کردند و بدون اینکه تیری بیفکنند تسلیم شدند. وقتی دشمن هنوز دور بود مردم با هم گریختند و اسیر گردیدند. 3
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
پس مرا به حال خود بگذارید تا برای مصیبت قومم، به تلخی بگریم. کوشش نکنید مرا تسلی دهید، 4
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
زیرا اینک زمان آن رسیده که خداوند، خداوند لشکرهای آسمان اورشلیم را دچار مصیبت و آشفتگی و انهدام کند. دیوارهای شهر ما فرو ریخته است. فریاد مردم در کوهها طنین می‌افکند. 5
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
سپاهیان عیلام تیر و کمان را آماده کرده، بر اسبهای خود سوار شده‌اند و سربازان سرزمین «قیر» سپرهای خود را به دست گرفته‌اند. 6
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
دشتهای سرسبز یهودا از ارابه‌های دشمن پر شده است و سواران دشمن به پشت دروازه‌های شهر رسیده‌اند. 7
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
نیروی دفاعی یهودا در هم شکسته است. برای آوردن اسلحه به اسلحه‌خانه می‌دوید. 8
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
رخنه‌های حصار شهر داوود را بررسی می‌کنید، سپس خانه‌های اورشلیم را می‌شمارید تا آنها را خراب کنید و مصالحشان را برای تعمیر حصار به کار ببرید. برای ذخیره کردن آب، 9
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
آب انبار در داخل شهر درست می‌کنید تا آب برکهٔ قدیمی تحتانی را در آن بریزید. تمام این کارها را می‌کنید اما به خدا که سازندهٔ همه چیز است توجهی ندارید. 11
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
خداوند، خداوند لشکرهای آسمان از شما می‌خواهد که گریه و ماتم کنید، موی خود را بتراشید و پلاس بپوشید. 12
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
اما شما شادی می‌کنید، گاو و گوسفند سر می‌برید تا گوشتشان را با شراب بخورید و خوش بگذرانید. می‌گویید: «بیاید بخوریم و بنوشیم، چون فردا می‌میریم.» 13
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
خداوند لشکرهای آسمان به من گفته که این گناه شما تا به هنگام مرگ هرگز آمرزیده نخواهد شد. بله، این را خداوند لشکرهای آسمان فرموده است. 14
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
خداوند، خداوند لشکرهای آسمان به من فرمود که نزد «شبنا» وزیر دربار بروم و به او چنین بگویم: 15
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
«تو در اینجا چه می‌کنی؟ چه کسی به تو اجازه داده در اینجا قبری برای خود بکنی؟ ای کسی که قبر خود را در این صخرۀ بلند می‌تراشی، 16
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
هر مقامی که داشته باشی، خداوند تو را برمی‌دارد و دور می‌اندازد. 17
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
تو را مانند یک گوی برمی‌دارد و به سرزمینی دور پرتاب می‌کند. در آنجا تو در کنار ارابه‌هایت که به آنها افتخار می‌کردی خواهی مرد. تو مایهٔ ننگ دربار هستی، 18
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
پس خداوند تو را از این مقام و منصبی که داری برکنار خواهد کرد.» 19
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
خداوند به شبنا چنین می‌گوید: «در آن روز، خدمتگزار خود، اِلیاقیم، پسر حلقیا را به جای تو خواهم نشاند. 20
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
لباس تو را به او خواهم پوشاند و کمربندت را به کمرش خواهم بست و اقتدار تو را به او خواهم داد. او برای مردم اورشلیم و خاندان یهودا پدر خواهد بود. 21
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
کلید دربار داوود پادشاه را به او خواهم داد و او هر دری را بگشاید کسی آن را نخواهد بست و هر دری را ببندد کسی آن را نخواهد گشود! 22
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
او را مانند میخی، محکم در جای خود خواهم کوبید و او مایهٔ سربلندی خاندان خود خواهد شد. 23
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
«اما تمام خاندان و فرزندان او مانند کاسه‌ها و کوزه‌هایی که بر میخ می‌آویزند بر او خواهند آویخت. 24
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
وقتی چنین شود آن میخی که محکم به دیوار کوبیده شده است، شل شده، خواهد افتاد و باری که بر آن است متلاشی خواهد شد.» این را خداوند لشکرهای آسمان فرموده است. 25
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.

< اشعیا 22 >