< اشعیا 20 >
سرگن، پادشاه آشور، سردار سپاه خود را به شهر اشدود در فلسطین فرستاد و آن را تسخیر کرد. | 1 |
A shekarar da babban shugaban yaƙin da Sargon sarkin Assuriya ya aika, ya zo Ashdod ya kuma fāɗa mata ya kuma ci ta da yaƙi,
سه سال پیش از این رویداد، خداوند به اشعیا پسر آموص فرموده بود که لباس و کفش خود را از تن در بیاورد و عریان و پا برهنه راه برود، و اشعیا چنین کرد. | 2 |
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
هنگامی که اشدود به دست آشور افتاد خداوند فرمود: «خدمتگزار من اشعیا مدت سه سال عریان و پا برهنه راه رفته است. این نشانهٔ بلاهای هولناکی است که من بر مصر و حبشه خواهم آورد. | 3 |
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kamar dai yadda bawana Ishaya ya yi ta yawo tsirara kuma ba takalmi a ƙafa shekara uku, a matsayin alama da shaida a kan Masar da Kush,
پادشاه آشور مردم مصر و حبشه را اسیر خواهد کرد و کوچک و بزرگ را مجبور خواهد ساخت عریان و پا برهنه راه بروند تا مصر را رسوا کند. | 4 |
haka sarkin Assuriya zai kwashe kamammun Masarawa da Kushawa tsirara kuma ba takalma a ƙafa, yaro da babba, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar.
آنگاه مردمی که در سواحل فلسطین زندگی میکنند و تکیهگاهشان حبشه، و فخرشان مصر است، پریشان و رسوا شده، خواهند گفت:”اگر بر سر مصر که میخواستیم از دست آشور به او پناه ببریم چنین بلایی آمد، پس بر سر ما چه خواهد آمد؟“» | 5 |
Waɗanda suka dogara ga Kush suka yi taƙama da Masar za su ji tsoro su kuma sha kunya.
A wannan rana mutanen da suke zama a bakin teku za su ce, ‘Dubi abin da ya faru da waɗanda muka dogara a kai, waɗanda muka gudu muka je don neman taimako da ceto daga sarkin Assuriya! Yaya za mu tsira?’”