< اشعیا 15 >

این است پیغام خدا برای سرزمین موآب: شهرهای عار و قیرِ موآب در یک شب ویران می‌شوند. 1
Abin da Allah ya yi magana a kan Mowab shi ne, An lalatar da Ar a Mowab, an hallaka ta da dare! An lalatar da Kir a Mowab, an hallaka ta da dare!
در دیبون قوم عزادار موآب به بتخانه‌ها پناه می‌برند تا برای شهرهای نبو و میدبا گریه کنند. همهٔ مردم موی سر و ریش خود را تراشیده، 2
Dibon ya haura zuwa haikalinta, zuwa masujadan kan tudu don tă yi kuka; Mowab ta yi ihu a kan Nebo da Medeba. An aske kowane kai an kuma yanke kowane gemu.
لباس عزا پوشیده‌اند و در کوچه‌ها راه می‌روند. از هر خانه‌ای صدای شیون و زاری بلند است. 3
A tituna sun sa tsummoki a jikunansu; a kan rufin ɗakuna da kuma dandalin taruwa dukansu sai makoki suke yi, sun kwanta suna kuka.
صدای گریهٔ شهرهای حشبون و العاله تا یاهص نیز شنیده می‌شود. حتی جنگاوران موآب نیز ناله می‌کنند و از شدت ترس می‌لرزند. 4
Heshbon da Eleyale sun yi kuka da ƙarfi, aka ji muryoyinsu ko’ina har zuwa Yahaz. Saboda haka mayaƙan Mowab suka yi kuka da ƙarfi, har zuciyarsu ta karai.
دلم برای موآب نالان است. مردم موآب به صوغر و عجلت شلشیا فرار می‌کنند؛ با گریه از گردنهٔ لوحیت بالا می‌روند؛ صدای نالهٔ ایشان در طول راه حورونایم به گوش می‌رسد. 5
Zuciyata ta yi kuka a kan Mowab; mutanenta sun gudu har zuwa Zowar, har zuwa Eglat Shelishiya. Sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka; a kan hanyar zuwa Horonayim suna makoki saboda hallakawarsu.
رودخانهٔ نمریم خشک شده است! علف سرسبز کنار رودخانه‌ها پلاسیده و نهالها از بین رفته‌اند. 6
Ruwayen Nimrim sun ƙafe ciyayin kuma sun bushe; tsire-tsire duk sun ɓace babu sauran ɗanyen abu.
مردم اندوختهٔ خود را برمی‌دارند تا از راه درهٔ بیدها فرار کنند. 7
Saboda haka dukiyar da suka tara suka kuma ajiye sun ɗauka suka ƙetare Rafin Arabim da su.
شیون موآب در مرزهای آن طنین افکنده است و صدای زاری آن تا به اجلایم و بئرایلیم رسیده است. 8
Ƙugin kukansu ya kai ko’ina a iyakar Mowab; kururuwarsu ta kai har zuwa Eglayim, makokinsu ya kai har zuwa Beyer-Elim.
رودخانهٔ دیمون از خون سرخ شده است، ولی خدا باز هم اهالی دیمون را مجازات خواهد کرد. بازماندگان و فراریان موآب نیز جان به در نخواهند برد و طعمهٔ شیر خواهند شد. 9
Ruwayen Dimon sun cika da jini, amma zan yi ƙari a kan Dimon, zan kawo zaki a kan masu gudu na Mowab da kuma a kan waɗanda suka ragu a ƙasar.

< اشعیا 15 >