< اشعیا 12 >

در آن روز، اسرائیل این سرود را خواهد خواند: «ای خداوند، تو را شکر می‌کنم، زیرا بر من غضبناک بودی، اما اینک مرا تسلی می‌دهی و دیگر غضبناک نیستی. 1
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
براستی خدا نجا‌ت‌دهندۀ من است؛ بر او توکل خواهم کرد و نخواهم ترسید. خداوند یهوه قوت و سرود من است؛ او نجات من است.» 2
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
پس با شادمانی از چشمه‌های نجات آب خواهید کشید، 3
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
و در آن روز خواهید گفت: «خداوند را شکر کنید! نام او را ستایش نمایید! اعمال او را به دنیا اعلام کنید! بگویید که او عظیم است! 4
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
برای خداوند سرود بسرایید، زیرا کارهای بزرگی انجام داده است. بگذارید تمام جهان بداند که او چه کرده است. 5
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
بگذارید مردم اورشلیم فریاد شادی سر دهند، زیرا خدای قدوس اسرائیل عظیم است و در میان قومش حضور دارد.» 6
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”

< اشعیا 12 >