< اشعیا 11 >
کُندۀ خاندان داوود جوانه خواهد زد! بله، از ریشهٔ کهنۀ آن شاخهای تازه میوه خواهد داد. | 1 |
Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
روح خداوند بر آن شاخه قرار خواهد گرفت، یعنی روح حکمت و فهم، روح مشورت و قوت، و روح شناخت و ترس از خداوند. | 2 |
Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
تمام خوشی او در اطاعت از خداوند خواهد بود. او بر اساس آنچه دیده یا شنیده میشود داوری نخواهد کرد؛ | 3 |
zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
بلکه از حق فقرا و مظلومان دفاع خواهد کرد. جهان را به عصای دهانش خواهد زد و بدکاران را به نَفَس لبهایش هلاک خواهد کرد. | 4 |
amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
عدالت را همچون کمربند به کمر خواهد بست و حقیقت را مانند شال کمر. | 5 |
Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
در آن زمان گرگ و بره در کنار هم به سر خواهند برد، پلنگ و بزغاله با هم خواهند خوابید، گوساله با شیر راه خواهد رفت؛ و یک کودک آنها را به هر جا که بخواهد، خواهد راند. | 6 |
Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
گاو در کنار خرس خواهد چرید، بچه خرس و گوساله در کنار هم خواهند خوابید، و شیر مانند گاو علف خواهد خورد. | 7 |
Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
بچهٔ شیرخوار در میان مارها، بدون خطر بازی خواهد کرد؛ و طفلی که از شیر گرفته شده باشد دست خود را داخل لانهٔ افعی خواهد کرد بیآنکه آسیب ببیند. | 8 |
Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
هیچ بدی و گزندی در کوه مقدّس خدا وجود نخواهد داشت، زیرا همانگونه که دریا از آب پر است همچنان جهان از شناخت خداوند پر خواهد شد. | 9 |
Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
در آن روز، وارث تخت داوود پرچم نجاتی برای تمام قومها خواهد بود و مردم به سوی او خواهند آمد و سرزمین او از شکوه و جلال پر خواهد شد. | 10 |
A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
در آن زمان خداوند بار دیگر دست خود را دراز خواهد کرد و بازماندگان قوم خود را از آشور، مصر، سودان، حبشه، عیلام، بابِل، حمات، و از تمام جزایر و بنادر دور دست به اسرائیل باز خواهد آورد. | 11 |
A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
او در میان قومها پرچمی برخواهد افراشت و مردم اسرائیل و یهودا را که پراکنده شدهاند، از گوشه و کنار دنیا جمع خواهد کرد. | 12 |
Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
سرانجام دشمنی و کینهای که میان اسرائیل و یهودا بود از بین خواهد رفت و آن دو دیگر با هم نخواهند جنگید. | 13 |
Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
آنان با هم متحد شده، بر فلسطینیان که در غرب هستند یورش خواهند برد و اقوامی را که در شرق سکونت دارند غارت خواهند کرد. سرزمین ادوم و موآب را تصرف خواهند کرد و سرزمین عمون را مطیع خود خواهند ساخت. | 14 |
Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
خداوند خلیج دریای مصر را خشک خواهد ساخت و دست خود را بر رود فرات بلند خواهد کرد و باد تندی خواهد فرستاد تا آن را به هفت نهر تقسیم کند؛ آنگاه مردم را از آن خشکی عبور خواهد داد. | 15 |
Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
برای بازماندگان قوم او در آشور شاهراهی خواهد بود تا آنان مانند اجداد خود که از مصر بیرون آمدند، به سرزمین خود بازگردند. | 16 |
Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.