< اشعیا 1 >

این کتاب شامل رؤیاهایی است که اشعیا پسر آموص دربارهٔ یهودا و پایتخت آن اورشلیم دید. او این رؤیاها را در دوران سلطنت عُزیا، یوتام، آحاز و حِزِقیا، پادشاهان سرزمین یهودا دید. 1
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
ای آسمان و زمین، به آنچه خداوند می‌فرماید گوش کنید: «فرزندان پروردم و بزرگ کردم، اما آنها بر ضد من برخاستند. 2
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
گاو مالک خود را و الاغ صاحب خویش را می‌شناسد، اما قوم من فهم ندارد و اسرائیل خدای خود را نمی‌شناسد.» 3
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
وای بر شما قوم گناهکار که پشتتان زیر بار گناهانتان خم شده است. وای بر شما مردم شرور و فاسد که از خداوند، قدوس اسرائیل روگردانده و او را ترک گفته‌اید. 4
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
چرا باز کاری می‌کنید که صدمه ببینید؟ آیا به اندازهٔ کافی مجازات نشده‌اید؟ ای اسرائیل، فکر و دلت تماماً بیمار است. 5
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
از سر تا پا مجروح و مضروب هستی؛ جای سالم در بدنت نمانده است. زخمهایت باز مانده و عفونی شده، کسی آنها را بخیه نزده و مرهم نمالیده است. 6
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
ای قوم اسرائیل، سرزمینتان ویران گشته و شهرهایتان به آتش کشیده شده است. بیگانگان در برابر چشمانتان سرزمینتان را غارت می‌کنند و آنچه می‌بینند به نابودی می‌کشند. 7
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
اورشلیم همچون کلبه‌ای در تاکستان و مانند آلونکی در بوستان خیار، بی‌دفاع و تنها مانده است. 8
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
اگر خداوند لشکرهای آسمان باقیماندگانی برایمان نمی‌گذاشت مانند اهالی سدوم و عموره به کلی از بین رفته بودیم. 9
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
ای حاکمان و ای مردم اورشلیم که چون اهالی سدوم و عموره فاسد هستید، به کلام خداوند گوش دهید. 10
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
او می‌فرماید: «از قربانیهای شما بیزارم. دیگر قربانیهای سوختنی به حضور من نیاورید. قوچهای فربهٔ شما را نمی‌خواهم. دیگر مایل نیستم خون گاوها و بره‌ها و بزغاله‌ها را ببینم. 11
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
چه کسی از شما خواسته که وقتی به حضور من می‌آیید این قربانیها را با خود بیاورید؟ چه کسی به شما اجازه داده که اینچنین آستان خانهٔ مرا پایمال کنید؟ 12
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
دیگر این هدایای باطل را نیاورید. من از بخوری که می‌سوزانید نفرت دارم و از اجتماعات مذهبی و مراسمی که در اول ماه و در روز شَبّات بجا می‌آورید بیزارم. نمی‌توانم این اجتماعات گناه‌آلود را تحمل کنم. 13
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
از جشنهای ماه نو و اعیاد مذهبی شما متنفرم و تحمل دیدن هیچ‌کدام را ندارم. 14
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
هرگاه دستهایتان را به سوی آسمان دراز کنید، روی خود را از شما برخواهم گرداند و چون دعای بسیار کنید، اجابت نخواهم نمود؛ زیرا دستهای شما به خون آلوده است. 15
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
«خود را بشویید و طاهر شوید! گناهانی را که در حضور من مرتکب شده‌اید از خود دور کنید. 16
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
نیکوکاری را بیاموزید و با انصاف باشید. به ستمدیدگان کمک کنید، به داد یتیمان برسید و از حق بیوه‌زنان دفاع کنید.» 17
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
خداوند می‌فرماید: «بیایید این موضوع را بین خود حل کنیم: اگرچه لکه‌های گناهانتان به سرخی خون باشد، اما من آنها را مانند پشم پاک می‌کنم و شما را همچون برف سفید می‌سازم! 18
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
کافی است مرا اطاعت کنید تا شما را از محصول زمین سیر کنم. 19
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
اما اگر به سرپیچی از من ادامه دهید، به دم شمشیر دشمن کشته خواهید شد.» این کلام خداوند است. 20
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
ای اورشلیم، زمانی تو نسبت به خداوند وفادار بودی، اما اینک همچون یک فاحشه به دنبال خدایان دیگر می‌روی. زمانی شهر عدل و انصاف بودی، اما اکنون شهر جنایتکاران شده‌ای. 21
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
زمانی چون نقره خالص بودی، ولی اینک فلزی بی‌مصرف شده‌ای. زمانی همچون شراب ناب بودی، ولی اکنون با شرابی آمیخته با آب شده‌ای. 22
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
رهبرانت شورشگر و شریک دزدانند؛ همه رشوه‌خوارند و هدیه می‌گیرند؛ از یتیمان حمایت نمی‌کنند و به دادخواهی بیوه‌زنان گوش نمی‌دهند. 23
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
بنابراین خداوند، خداوند لشکرهای آسمان، خداوند متعال اسرائیل، به آنها می‌گوید: «شما دشمن من هستید؛ تا از شما انتقام نگیرم آرام نمی‌شوم. 24
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
دست خود را به ضد شما بلند می‌کنم و شما را مثل فلز در کوره می‌گدازم تا از ناخالصی خود پاک شوید. 25
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
«مانند گذشته، رهبران و مشاورانی لایق به شما خواهم بخشید تا اورشلیم را به شهر عدالت و امانت مشهور سازند.» 26
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
صَهیون به انصاف نجات خواهد یافت و اهالی توبه‌کار آن به عدالت احیا خواهند شد. 27
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
اما گناهکاران و عصیانگران را به هلاکت خواهد رساند و کسانی را که او را ترک کنند نابود خواهد کرد. 28
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
شما از بت‌پرستی خود در زیر درختان بلوط باغهایتان خجل و شرمسار خواهید شد، 29
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
و مانند بلوطی خشک و باغی بی‌آب، از بین خواهید رفت. 30
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
مردان زورمند شما با اعمالشان مانند کاه در آتش خواهند سوخت و کسی قادر نخواهد بود آنها را نجات دهد. 31
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< اشعیا 1 >