< حَجَّی 2 >

در روز بیست و یکم ماه هفتم همان سال، خداوند به حَجَّی گفت: 1
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
«اکنون با زَروبابِل فرزند شِئَلتیئیل، فرماندار یهودا، یِهوشَع فرزند یِهوصاداق، کاهن اعظم، و نیز با تمامی باقیماندگان قوم سخن بگو و از ایشان بپرس: 2
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
”آیا کسی در بین شما هست که شکوه و عظمت خانهٔ خدا را آن طوری که در سابق بود به خاطر آورد؟ آیا این خانه‌ای که می‌سازید در مقایسه با خانهٔ قبلی به نظر شما ناچیز نمی‌آید؟ 3
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
اما اکنون خداوند می‌فرماید: هر چند به ظاهر چنین است اما مأیوس نشوید. ای زروبابِل و یهوشع و همهٔ قوم، قوی دل باشید و کار کنید، چون من با شما هستم. این را خداوند لشکرهای آسمان می‌گوید. 4
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
وقتی از مصر بیرون می‌آمدید به شما وعده دادم که روح من در میان شما می‌ماند؛ پس ترسان نباشید!“ 5
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
«زیرا خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: بار دیگر آسمانها و زمین، دریاها و خشکی را به لرزه درمی‌آورم. 6
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
تمام قومها را سرنگون می‌کنم، و ثروت آنها به این خانه سرازیر می‌شود. و خداوند لشکرهای آسمان می‌گوید: من این مکان را با جلال خود پر می‌سازم. 7
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: تمام طلا و نقرهٔ دنیا از آن من است. 8
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
خداوند لشکرهای آسمان می‌گوید: شکوه و عظمت آیندهٔ این خانه از شکوه و عظمت خانهٔ قبلی بیشتر خواهد بود و در این مکان به قوم خود صلح و سلامتی خواهم بخشید.» این است آنچه خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید. 9
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
در روز بیست و چهارم ماه نهم از دومین سال سلطنت داریوش، این پیام از جانب خداوند به حَجَّی نبی نازل شد: 10
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
«خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: از کاهنان بخواه تا جواب شرعی این سؤال را بدهند: 11
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
”اگر کسی قسمتی از گوشت مقدّس قربانی را در دامن ردایش گذاشته آن را حمل کند و برحسب اتفاق ردایش با نان، آش، شراب، روغن و یا هر نوع خوراک دیگری تماس پیدا کند، آیا آن خوراک مقدّس می‌شود؟“» کاهنان جواب دادند: «نه، مقدّس نمی‌شود؟» 12
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
سپس حَجَّی پرسید: «و اما اگر شخصی به جسد مرده‌ای دست بزند و بدین ترتیب نجس شود و بعد به یکی از این خوراکها دست بزند، آیا آن خوراک نجس می‌شود؟» کاهنان جواب دادند: «بلی، نجس می‌شود.» 13
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
پس حَجَّی گفت: «خداوند می‌فرماید شما نیز در نظر من همین‌طور نجس هستید و هر کاری که می‌کنید و هر قربانی که به خانۀ من می‌آورید، نجس است. 14
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
خوب فکر کنید و ببینید قبل از اینکه دست به کار ساختن خانهٔ خداوند بزنید وضع شما چگونه بود. 15
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
در آن روزها وقتی انتظار داشتید دو خروار محصول برداشت کنید، فقط نصف آن به دستتان می‌رسید، و هنگامی که به امید پنجاه لیتر شراب به سراغ خمره‌هایتان می‌رفتید، بیشتر از بیست لیتر نمی‌یافتید. 16
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
من محصولات شما را با باد سوزان، آفت و تگرگ از بین بردم، اما با وجود همهٔ اینها به سوی من بازگشت نکردید. 17
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
ولی از امروز که روز بیست و چهارم ماه نهم و روزی است که بنیاد خانهٔ خدا گذاشته شده است، ببینید من برای شما چه خواهم کرد. 18
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
اگرچه غله‌ای در انبارها باقی نمانده، و هنوز درختان انگور، انجیر، انار و زیتون میوه نداده‌اند، ولی من به شما برکت خواهم داد.» 19
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
در همان روز پیام دیگری از جانب خداوند به حَجَّی رسید: 20
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
«به زروبابِل، حاکم یهودا بگو که به‌زودی آسمانها و زمین را به لرزه درمی‌آورم، 21
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
تختهای فرمانروایان را واژگون می‌سازم و قدرت آنان را از بین می‌برم. ارابه‌ها و سواران را سرنگون می‌کنم، و اسبها کشته می‌شوند و سوارانشان یکدیگر را با شمشیر از پای در می‌آورند. 22
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
«خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید: وقتی که این امور واقع گردد، ای زروبابِل، خدمتگزار من، تو برای من مانند نگین انگشتر خواهی بود، زیرا تو را برگزیده‌ام.» این است آنچه خداوند لشکرهای آسمان می‌فرماید. 23
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< حَجَّی 2 >