< پیدایش 9 >

خدا، نوح و پسرانش را برکت داد و به ایشان فرمود: «بارور و زیاد شوید و زمین را پُر سازید. 1
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
همهٔ حیوانات و خزندگان زمین، پرندگان هوا و ماهیان دریا از شما خواهند ترسید، زیرا همهٔ آنها را زیر سلطهٔ شما قرار داده‌ام. 2
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
من آنها را برای خوراک به شما داده‌ام، همان‌طور که گیاهان سبز را به شما بخشیدم. 3
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
اما گوشت را با خونش که بدان حیات می‌بخشد نخورید. 4
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
و من تاوان خون شما را باز می‌ستانم. آن را از هر جانوری باز می‌ستانم. تاوان جان انسان را از دست همنوعش نیز باز می‌ستانم. 5
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
هر که خون انسانی را بریزد، خون او نیز به دست انسان ریخته خواهد شد؛ زیرا خدا انسان را به صورت خود آفرید. 6
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
و اما شما، فرزندان زیاد تولید کنید و زمین را پُر سازید.» 7
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
سپس خدا به نوح و پسرانش فرمود: 8
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
«من با شما و با نسلهای آیندهٔ شما عهد می‌بندم، 9
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
و نیز با تمام حیواناتی که با شما در کشتی بودند یعنی همۀ پرندگان، چارپایان و جانوران. 10
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
بله، من با شما عهد می‌بندم که بعد از این هرگز موجودات زنده را به‌وسیلۀ طوفان هلاک نکنم و زمین را نیز دیگر بر اثر طوفان خراب ننمایم. 11
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
این است نشان عهد جاودانی من: 12
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
رنگین‌کمان خود را در ابرها می‌گذارم و این نشان عهدی خواهد بود که من با جهان بسته‌ام. 13
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
وقتی ابرها را بالای زمین بگسترانم و رنگین‌کمان دیده شود، 14
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
آنگاه قولی را که به شما و تمام جانداران داده‌ام به یاد خواهم آورد و دیگر هرگز تمام موجودات زنده به‌وسیلهٔ طوفان هلاک نخواهند شد. 15
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
وقتی رنگین‌کمان را در ابرها ببینم، عهد جاودانی میان خدا و هر موجود زنده بر زمین را به یاد خواهم آورد.» 16
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
سپس خدا به نوح گفت: «این رنگین‌کمان نشان عهدی است که من با تمام موجودات زندهٔ روی زمین می‌بندم.» 17
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
سه پسر نوح که از کشتی خارج شدند، سام و حام و یافث بودند. (حام پدر قوم کنعان است.) 18
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
همه قومهای دنیا از سه پسر نوح به وجود آمدند. 19
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
نوح به کار کشاورزی مشغول شد و تاکستانی غرس نمود. 20
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
روزی که شراب زیاد نوشیده بود، در حالت مستی در خیمه‌اش برهنه خوابید. 21
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
حام، پدر کنعان، برهنگی پدر خود را دید و بیرون رفته به دو برادرش خبر داد. 22
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
سام و یافث با شنیدن این خبر، ردایی روی شانه‌های خود انداخته عقب‌عقب به طرف پدرشان رفتند تا برهنگی او را نبینند. سپس او را با آن ردا پوشانیدند. 23
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
وقتی نوح به حال عادی برگشت و فهمید که حام چه کرده است، 24
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
گفت: «کنعان ملعون باد. برادران خود را بندهٔ بندگان باشد.» 25
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
و نیز گفت: «متبارک باد یهوه، خدای سام! کنعان بندهٔ او باشد. 26
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
خدا زمین یافث را وسعت بخشد، و او را شریک سعادت سام گرداند، و کنعان بندهٔ او باشد.» 27
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
پس از طوفان، نوح ۳۵۰ سال دیگر عمر کرد 28
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
و در سن ۹۵۰ سالگی وفات یافت. 29
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.

< پیدایش 9 >