< پیدایش 21 >
خداوند به وعدهای که به سارا داده بود، وفا کرد. | 1 |
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
سارا در زمانی که خداوند مقرر فرموده بود، حامله شد و برای ابراهیم در سن پیری پسری زایید. | 2 |
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
ابراهیم پسرش را که سارا برای او به دنیا آورده بود، اِسحاق (یعنی «خنده») نام نهاد؛ | 3 |
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
و ابراهیم طبق فرمان خدا اسحاق را هشت روز بعد از تولدش ختنه کرد. | 4 |
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
هنگام تولدِ اسحاق، ابراهیم صد ساله بود. | 5 |
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
سارا گفت: «خدا برایم خنده و شادی آورده است. هر کس خبر تولد پسرم را بشنود با من خواهد خندید. | 6 |
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
چه کسی باور میکرد که روزی من بچهٔ ابراهیم را شیر بدهم؟ ولی اکنون برای ابراهیم در سن پیری او پسری زاییدهام!» | 7 |
Ta kuma ƙara da cewa, “Dā, wa zai iya ce wa Ibrahim, Saratu za tă yi renon yara? Duk da haka na haifar masa ɗa cikin tsufansa.”
اسحاق بزرگ شده، از شیر گرفته شد و ابراهیم به این مناسبت جشن بزرگی بر پا کرد. | 8 |
Yaron ya yi girma, aka kuma yaye shi, a ranar da aka yaye shi kuwa, Ibrahim ya yi babban biki.
یک روز سارا متوجه شد که اسماعیل، پسر هاجر مصری، اسحاق را اذیت میکند. | 9 |
Amma Saratu ta ga cewa yaron da Hagar, mutuniyar Masar ta haifa wa Ibrahim yana wa ɗanta Ishaku gori,
پس به ابراهیم گفت: «این کنیز و پسرش را از خانه بیرون کن، زیرا اسماعیل با پسر من اسحاق وارث تو نخواهد بود.» | 10 |
sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori baiwan nan tare da ɗanta, saboda ɗan baiwan nan ba zai taɓa raba gādo da ɗana Ishaku ba.”
این موضوع ابراهیم را بسیار رنجاند، چون اسماعیل نیز پسر او بود. | 11 |
Al’amarin ya ɓata wa Ibrahim rai sosai domin zancen ya shafi ɗansa.
اما خدا به ابراهیم فرمود: «دربارهٔ پسر و کنیزت آزردهخاطر نشو. آنچه سارا گفته است انجام بده، زیرا توسط اسحاق است که تو صاحب نسلی میشوی که وعدهاش را به تو دادهام. | 12 |
Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada hankalinka yă tashi game da yaron nan da kuma baiwarka. Ka saurari duk abin da Saratu ta faɗa maka, saboda ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.
از پسر آن کنیز هم قومی به وجود خواهم آورد، چون او نیز پسر توست.» | 13 |
Zan ba ɗan baiwan nan al’umma shi ma, domin shi zuriyarka ne.”
پس ابراهیم صبح زود برخاست و نان و مشکی پُر از آب برداشت و بر دوش هاجر گذاشت، و او را با پسر روانه ساخت. هاجر به بیابان بئرشِبَع رفت و در آنجا سرگردان شد. | 14 |
Kashegari da sassafe sai Ibrahim ya ɗauki abinci da salkar ruwa, ya ba wa Hagar. Ya ɗora su a kafaɗunta, sa’an nan ya sallame ta da yaron. Ta kama hanyarta ta kuma yi ta yawo a cikin jejin Beyersheba.
وقتی آب مشک تمام شد، هاجر پسرش را زیر بوتهها گذاشت | 15 |
Sa’ad da ruwan da yake cikin salkan ya ƙare, sai ta ajiye yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace.
و خود حدود صد متر دورتر از او نشست و با خود گفت: «نمیخواهم ناظر مرگ فرزندم باشم.» و زارزار بگریست. | 16 |
Sai ta tafi, ta zauna ɗan nesa da yaron, misalin nisan harbin baka, gama ta yi tunani ta ce, “Ba zan iya kallon yaron yana mutuwa ba.” Da ta zauna nesa da yaron, sai ta fara kuka.
آنگاه خدا به نالههای پسر توجه نمود و فرشتهٔ خدا از آسمان هاجر را ندا داده، گفت: «ای هاجر، چه شده است؟ نترس! زیرا خدا نالههای پسرت را شنیده است. | 17 |
Allah kuwa ya ji yaron yana kuka, sai mala’ikan Allah ya kira Hagar daga sama ya ce mata, “Mene ne damuwarki, Hagar? Kada ki ji tsoro, Allah ya ji yaron yana kuka yayinda yake kwance a can.
برو و او را بردار و در آغوش بگیر. من قوم بزرگی از او به وجود خواهم آورد.» | 18 |
Ki ɗaga yaron ki riƙe shi a hannu, gama zan mai da shi al’umma mai girma.”
سپس خدا چشمان هاجر را گشود و او چاه آبی در مقابل خود دید. پس به طرف چاه رفته، مشک را پر از آب کرد و به پسرش نوشانید. | 19 |
Sa’an nan Allah ya buɗe idanunta ta ga wata rijiyar ruwa. Don haka sai ta tafi ta cika salkan da ruwa, ta kuma ba wa yaron ruwa ya sha.
و خدا با اسماعیل بود و او در صحرا بزرگ شده، در تیراندازی ماهر گشت. | 20 |
Allah ya kasance da yaron, yayinda yake girma. Ya yi zama a jeji, ya kuma zama maharbi.
او در صحرای فاران زندگی میکرد و مادرش دختری از مصر برای او گرفت. | 21 |
Yayinda yake zama a Jejin Faran, sai mahaifiyarsa ta samo masa mata daga Masar.
در آن زمان ابیملکِ پادشاه، با فرماندهٔ سپاهش فیکول نزد ابراهیم آمده، گفت: «خدا در آنچه میکنی با توست! | 22 |
A lokacin nan Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka zo suka ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai a ko mene ne kake yi.
اکنون به نام خدا سوگند یاد کن که به من و فرزندان و نوادههای من خیانت نخواهی کرد و همانطوری که من با تو به خوبی رفتار کردهام، تو نیز با من و مملکتم که در آن ساکنی، به خوبی رفتار خواهی نمود.» | 23 |
Yanzu ka rantse mini a nan a gaban Allah cewa, ba za ka yaudare ni ko’ya’yana ko kuma zuriyata ba. Ka nuna mini alheri, kai da ƙasar da kake zama baƙunci kamar yadda na nuna maka.”
ابراهیم پاسخ داد: «سوگند میخورم چنانکه گفتید رفتار کنم.» | 24 |
Ibrahim ya ce, “Na rantse.”
سپس ابراهیم دربارهٔ چاهِ آبی که خدمتگزاران ابیملک به زور از او گرفته بودند، نزد وی شکایت کرد. | 25 |
Sa’an nan Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek game da rijiyar ruwan da bayin Abimelek suka ƙwace.
ابیملکِ پادشاه گفت: «این اولین باری است که راجع به این موضوع میشنوم و نمیدانم کدام یک از خدمتگزارانم در این کار مقصر است. چرا پیش از این به من خبر ندادی؟» | 26 |
Sai Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan ba. Ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba, sai yau.”
آنگاه ابراهیم، گوسفندان و گاوانی به ابیملک داد و با یکدیگر عهد بستند. | 27 |
Sai Ibrahim ya kawo tumaki da shanu ya ba wa Abimelek, sai su biyun suka yi yarjejjeniya.
سپس ابراهیم هفت بره از گله جدا ساخت. | 28 |
Ibrahim ya ware’yan raguna bakwai daga cikin garke,
پادشاه پرسید: «چرا این کار را میکنی؟» | 29 |
sai Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Mene ne ma’anar’yan raguna bakwai da ka keɓe?”
ابراهیم پاسخ داد: «اینها هدایایی هستند که من به تو میدهم تا همه بدانند که این چاه از آنِ من است.» | 30 |
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ka karɓi waɗannan’yan tumaki bakwai daga hannuna a matsayin shaida cewa ni ne na haƙa wannan rijiya.”
از آن پس این چاه، بئرشبع (یعنی «چاه سوگند») نامیده شد، زیرا آنها در آنجا با هم عهد بسته بودند. | 31 |
Saboda haka aka kira wurin Beyersheba, domin a nan ne su biyun suka yi rantsuwa.
آنگاه ابیملک و فیکول فرماندهٔ سپاهش به سرزمین خود فلسطین بازگشتند. | 32 |
Bayan da aka yi yarjejjeniya a Beyersheba, sai Abimelek da Fikol, komandan rundunoninsa suka koma ƙasar Filistiyawa.
ابراهیم در کنار آن چاه درخت گزی کاشت و خداوند، خدای ابدی را عبادت نمود. | 33 |
Sai Ibrahim ya shuka itacen tsamiya a Beyersheba, a can kuma ya kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami.
ابراهیم مدت زیادی در سرزمین فلسطین در غربت زندگی کرد. | 34 |
Ibrahim kuwa ya zauna a ƙasar Filistiyawa na dogon lokaci.