< پیدایش 13 >
ابرام با زن خود سارای و لوط و هر آنچه که داشت به نِگِب، در جنوبِ، کنعان کوچ کرد. | 1 |
Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
ابرام بسیار ثروتمند بود. او طلا و نقره و گلههای فراوانی داشت. | 2 |
Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
ابرام و همراهانش از نگب رهسپار شده، مرحله به مرحله، به سوی بیتئیل رفتند، و میان بیتئیل و عای، جایی که قبلاً اطراق کرده بودند، اردو زدند. | 3 |
Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
این همان جایی بود که قبلاً ابرام در آنجا مذبحی ساخت و نام خداوند را خواند. | 4 |
da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
لوط نیز گاوان و گوسفندان و غلامان زیادی داشت. | 5 |
Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
ابرام و لوط به علّت داشتن گلههای بزرگ نمیتوانستند با هم در یک جا ساکن شوند، زیرا برای گلههایشان چراگاه کافی وجود نداشت | 6 |
Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
و بین چوپانان ابرام و لوط نزاع در میگرفت. (در آن زمان کنعانیها و فرّزیها نیز در آن سرزمین ساکن بودند.) | 7 |
Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
پس ابرام به لوط گفت: «ما قوم و خویش هستیم، و چوپانان ما نباید با یکدیگر نزاع کنند. | 8 |
Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
مصلحت در این است که از هم جدا شویم. اینک دشتی وسیع پیش روی ماست. هر سمتی را که میخواهی انتخاب کن و من هم به سمت مقابل تو خواهم رفت. اگر به طرف چپ بروی، من به طرف راست میروم و اگر طرف راست را انتخاب کنی، من به سمت چپ میروم.» | 9 |
Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
آنگاه لوط نگاهی به اطراف انداخت و تمام دره رود اردن را از نظر گذراند. همهٔ آن سرزمین تا صوغر، چون باغ عدن و مصر سرسبز بود. (هنوز خداوند شهرهای سدوم و عموره را از بین نبرده بود.) | 10 |
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
لوط تمام درهٔ اردن را برگزید و به طرف شرق کوچ کرد. بدین طریق او و ابرام از یکدیگر جدا شدند. | 11 |
Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
پس ابرام در سرزمین کنعان ماند و لوط به طرف شهرهای درهٔ اردن رفت و در نزدیکی سدوم ساکن شد. | 12 |
Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
مردمان شهر سدوم بسیار فاسد بودند و نسبت به خداوند گناه میورزیدند. | 13 |
Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
بعد از جدا شدن لوط از ابرام، خداوند به ابرام فرمود: «با دقت به اطراف خود نگاه کن! | 14 |
Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
تمام این سرزمین را که میبینی، تا ابد به تو و نسل تو میبخشم. | 15 |
Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
نسل تو را مانند غبار زمین بیشمار میگردانم. | 16 |
Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
برخیز و در سراسر این سرزمین که آن را به تو میبخشم، بگرد.» | 17 |
Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
آنگاه ابرام برخاست و خیمهٔ خود را جمع کرده، به بلوطستانِ ممری که در حبرون است کوچ نمود. در آنجا ابرام برای خداوند مذبحی ساخت. | 18 |
Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.