< پیدایش 12 >
خداوند به ابرام فرمود: «ولایت، خانه پدری و خویشاوندان خود را رها کن و به سرزمینی که من تو را بدانجا هدایت خواهم نمود برو. | 1 |
Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
من تو را پدر امت بزرگی میگردانم. تو را برکت میدهم و نامت را بزرگ میسازم و تو مایه برکت خواهی بود. | 2 |
“Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
آنانی را که تو را برکت دهند، برکت خواهم داد، و آنانی را که تو را لعنت کنند، لعنت خواهم کرد. همه مردم دنیا از تو برکت خواهند یافت.» | 3 |
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
پس ابرام طبق دستور خداوند، روانه شد و لوط نیز همراه او رفت. ابرام هفتاد و پنج ساله بود که حران را ترک گفت. | 4 |
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
او همسرش سارای و برادرزادهاش لوط، غلامان و تمامی دارایی خود را که در حران به دست آورده بود، برداشت و به کنعان کوچ کرد. | 5 |
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
وقتی به کنعان رسیدند، در کنار بلوطِ موره واقع در شکیم خیمه زدند. در آن زمان کنعانیها در آن سرزمین ساکن بودند، | 6 |
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
آنگاه خداوند بر ابرام ظاهر شده، فرمود: «من این سرزمین را به نسل تو خواهم بخشید.» پس ابرام در آنجا مذبحی برای خداوند که بر او ظاهر شده بود، بنا کرد. | 7 |
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
سپس از آنجا کوچ کرده، به سرزمین کوهستانی که از طرف غرب به بیتئیل و از طرف شرق به عای ختم میشد، رفت. ابرام در آن محل خیمه زد و مذبحی برای خداوند بنا کرده، او را پرستش نمود. | 8 |
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
بدین ترتیب ابرام با توقفهای پیدرپی به سمت نِگب کوچ کرد. | 9 |
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
ولی در آن سرزمین قحطی شد، پس ابرام به مصر رفت تا در آنجا زندگی کند. | 10 |
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
وقتی به مرز سرزمین مصر نزدیک شدند، ابرام به همسرش گفت: «تو زن زیبایی هستی. | 11 |
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
وقتی مصریها تو را ببینند، خواهند گفت:”این زن اوست. او را بکشیم و زنش را تصاحب کنیم!“ | 12 |
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
پس به آنها بگو تو خواهر منی، تا به خاطر تو مرا نکشند و با من به مهربانی رفتار کنند.» | 13 |
Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
وقتی وارد مصر شدند، مردم آنجا دیدند که سارای زن زیبایی است. | 14 |
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
عدهای از درباریانِ فرعون، سارای را دیدند و در حضور فرعون از زیبایی او بسیار تعریف کردند. فرعون دستور داد تا او را به قصرش ببرند. | 15 |
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
آنگاه فرعون به خاطر سارای، هدایای فراوانی از قبیل گوسفند و گاو و شتر و الاغ و غلامان و کنیزان به ابرام بخشید. | 16 |
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
اما خداوند، فرعون و تمام افراد قصر او را به بلای سختی مبتلا کرد، زیرا سارای، زن ابرام را به قصر خود برده بود. | 17 |
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
فرعونْ ابرام را به نزد خود فرا خواند و به او گفت: «این چه کاری بود که با من کردی؟ چرا به من نگفتی که سارای زن توست؟ | 18 |
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
چرا او را خواهر خود معرفی کردی تا او را به زنی بگیرم؟ حال او را بردار و از اینجا برو.» | 19 |
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
آنگاه فرعون به مأموران خود دستور داد تا ابرام و همسرش را با نوکران و کنیزان و هر آنچه داشتند روانه کنند. | 20 |
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.