< حِزِقیال 39 >

«ای پسر انسان، باز دربارهٔ جوج پیشگویی کن و بگو:”ای جوج که پادشاه ماشک و توبال هستی، خداوند یهوه می‌گوید من بر ضد تو هستم. 1
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
تو را از راهی که می‌روی باز می‌گردانم و از شمال به طرف کوههای اسرائیل می‌آورم. 2
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
سلاحهای سپاهیانت را از دستهایشان می‌اندازم. 3
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
تو و تمام سپاه عظیمت در کوهها خواهید مرد. شما را نصیب لاشخورها و جانوران می‌گردانم. 4
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
در صحرا از پای در خواهید آمد. من که خداوند یهوه هستم این را گفته‌ام. 5
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
بر ماجوج و تمام هم‌پیمانانت که در سواحل در امنیت زندگی می‌کنند، آتش می‌بارانم و آنها خواهند دانست که من یهوه هستم.“ 6
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
«به این طریق نام قدوس خود را به قوم خود اسرائیل می‌شناسانم و دیگر اجازه نمی‌دهم که نام قدوس من بی‌حرمت شود. آنگاه قومها خواهند دانست که من یهوه، خدای قدوس قوم اسرائیل هستم.» 7
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
خداوند یهوه می‌گوید: «آن روز داوری خواهد رسید و همه چیز درست به همان طریقی که گفته‌ام اتفاق خواهد افتاد. 8
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
«ساکنان شهرهای اسرائیل از شهر خارج شده، تمام سلاحهای شما را یعنی سپرها، کمانها، تیرها، نیزه‌ها و چماقها را برای سوزاندن جمع خواهند کرد و این برای هیزم هفت سال کافی خواهد بود. 9
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
این سلاحهای جنگی تا هفت سال آتش آنها را تأمین خواهد کرد. از صحرا هیزم نخواهند آورد و از جنگل چوب نخواهند برید، چون این سلاحها احتیاج آنها را از لحاظ هیزم رفع خواهد کرد. قوم اسرائیل غارت‌کنندگان خود را غارت خواهند نمود.» خداوند یهوه این را فرموده است. 10
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
خداوند می‌فرماید: «من در اسرائیل در”وادی عابران“، که در شرق دریای مرده قرار دارد، برای جوج و تمام سپاهیان او گورستان بزرگی درست می‌کنم به طوری که راه عابران را مسدود خواهد ساخت. جوج و تمام سپاهیانش در آنجا دفن خواهند شد و نام آن وادی به”درهٔ سپاهیان جوج“تبدیل می‌گردد. 11
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
هفت ماه طول خواهد کشید تا قوم اسرائیل جنازه‌ها را دفن کنند و زمین را پاک سازند. 12
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
تمام اسرائیلی‌ها جمع خواهند شد و اجساد را دفن خواهند کرد. این روز پیروزی من، برای اسرائیل روزی فراموش نشدنی خواهد بود. 13
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
پس از پایان این هفت ماه، عده‌ای تعیین می‌شوند تا در سراسر زمین بگردند و اجسادی را که باقی مانده‌اند پیدا کنند و دفن نمایند تا زمین دوباره پاک شود. 14
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
هر وقت آنها استخوان انسانی را ببینند، علامتی کنارش می‌گذارند تا دفن‌کنندگان بیایند و آن را به درهٔ سپاهیان جوج ببرند و در آنجا دفن کنند. 15
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
(در آن محل شهری به نام این سپاهیان خواهد بود.) به این ترتیب، زمین بار دیگر پاک خواهد شد.» 16
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
خداوند یهوه به من فرمود: «ای پسر انسان، تمام پرندگان و جانوران را صدا کن و به آنها بگو که خداوند می‌گوید:”بیایید و قربانی‌ای را که برای شما آماده کرده‌ام بخورید. به کوههای اسرائیل بیایید و گوشت بخورید و خون بنوشید! 17
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
گوشت جنگاوران را بخورید و خون رهبران جهان را بنوشید که مانند قوچها، بره‌ها، بزها و گاوهای پرواری باشان ذبح شده‌اند. 18
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
آنقدر گوشت بخورید تا سیر شوید و آنقدر خون بنوشید تا مست گردید! این جشن قربانی را من برایتان ترتیب داده‌ام! 19
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
به مهمانی من بیایید و بر سر سفره‌ام گوشت اسبان، سواران و جنگاوران را بخورید! من که خداوند یهوه هستم این را می‌گویم.“ 20
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
«در میان قومها جلال و عظمت خود را به این طریق نشان خواهم داد. همه مجازات شدن جوج را خواهند دید و خواهند دانست که این کار من است. 21
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
قوم اسرائیل نیز خواهند دانست که من یهوه، خدای ایشان هستم. 22
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
قومها پی خواهند برد که قوم اسرائیل به سبب گناهان خود تبعید شده بودند، زیرا به خدای خود خیانت کرده بودند. پس من نیز روی خود را از آنان برگرداندم و گذاشتم دشمنانشان ایشان را نابود کنند. 23
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
رویم را از ایشان برگرداندم و آنان را به سزای گناهان و اعمال زشتشان رساندم.» 24
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
خداوند یهوه می‌فرماید: «ولی اینک به اسارت قوم خود پایان می‌دهم و بر ایشان رحم می‌کنم و غیرتی را که برای نام قدوس خود دارم نشان خواهم داد. 25
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
وقتی آنها بار دیگر در وطن خود دور از تهدید دیگران در امنیت ساکن شوند آنگاه دیگر به من خیانت نخواهند کرد و سرافکنده نخواهند شد. 26
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
آنان را از سرزمینهای دشمنانشان به وطن باز می‌گردانم و بدین ترتیب، به‌وسیلۀ ایشان به قومها نشان می‌دهم که من قدوس هستم. 27
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
آنگاه قوم من خواهند دانست که من یهوه، خدای ایشان هستم و این منم که آنان را به اسارت می‌فرستم و باز می‌گردانم و نمی‌گذارم حتی یک نفر از آنها در سرزمین بیگانه باقی بماند. 28
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
من روح خود را بر آنها می‌ریزم و دیگر هرگز روی خود را از ایشان برنمی‌گردانم. من که خداوند یهوه هستم این را گفته‌ام.» 29
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< حِزِقیال 39 >