< حِزِقیال 38 >
این پیغام نیز از جانب خداوند به من رسید: | 1 |
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان، رو به جوج از سرزمین ماجوج، حاکم قوم ماشک و توبال، بایست و بر ضد او پیشگویی کن. | 2 |
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
و بگو که خداوند یهوه چنین میفرماید: من بر ضد تو هستم. | 3 |
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
قلاب در چانهات میگذارم و تو را به سوی هلاکت میکشم. سربازان پیاده و سواران مسلح تو بسیج شده، سپاه بسیار بزرگ و نیرومندی تشکیل خواهند داد. | 4 |
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
پارس، کوش، و فوط هم با تمام سلاحهای خود به تو خواهند پیوست. | 5 |
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
تمام لشکر سرزمین جومِر و توجَرمه از شمال، و نیز بسیاری از قومهای دیگر، به تو ملحق خواهند شد. | 6 |
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
ای جوج، تو رهبر آنها هستی، پس آماده شو و تدارک جنگ ببین! | 7 |
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
«پس از یک مدت طولانی از تو خواسته خواهد شد که نیروهای خود را بسیج کنی. تو به سرزمین اسرائیل حمله خواهی کرد، سرزمینی که مردم آن از اسارت سرزمینهای مختلف بازگشته و در سرزمین خود در امنیت ساکن شدهاند؛ | 8 |
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
ولی تو و تمام همپیمانانت سپاهی بزرگ تشکیل خواهید داد و مثل طوفانی سهمگین بر آنها فرود خواهید آمد و مانند ابری سرزمین اسرائیل را خواهید پوشاند.» | 9 |
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
خداوند یهوه میفرماید: «در آن هنگام تو نقشههای پلیدی در سر خواهی پروراند؛ | 10 |
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
و خواهی گفت:”اسرائیل سرزمینی بیدفاع است و شهرهایش حصار ندارند! به جنگ آن میروم و این قوم را که در کمال امنیت و اطمینان زندگی میکنند، از بین میبرم! | 11 |
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
به آن شهرهایی که زمانی خراب بودند، ولی اینک آباد گشته و از مردمی پر شدهاند که از سرزمینهای دیگر بازگشتهاند، حمله میکنم و غنایم فراوان به دست میآورم. زیرا اکنون اسرائیل گاو و گوسفند و ثروت بسیار دارد و مرکز تجارت دنیاست.“ | 12 |
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
«مردم سبا و دِدان، و تجار تَرشیش به تو خواهند گفت:”آیا با سپاه خود آمدهای تا طلا و نقره و اموال ایشان را غارت کنی و حیواناتشان را با خود ببری؟“» | 13 |
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
خداوند یهوه به جوج میفرماید: «زمانی که قوم من در سرزمین خود در امنیت زندگی کنند، تو برمیخیزی و | 14 |
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
با سپاه عظیم خود از شمال میآیی و مثل ابر زمین را میپوشانی. این، در آیندهٔ دور اتفاق خواهد افتاد. من تو را به جنگ سرزمین خود میآورم، ولی بعد در برابر چشمان همه قومها تو را از میان برمیدارم تا به همهٔ آنها قدوسیت خود را نشان دهم و تا آنها بدانند که من خدا هستم.» | 15 |
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
خداوند یهوه میفرماید: «تو همانی که مدتها پیش توسط خدمتگزارانم یعنی انبیای اسرائیل در بارهات پیشگویی کرده، گفتم که بعد از آنکه سالهای بسیار بگذرد، تو را به جنگ قوم خود خواهم آورد. | 17 |
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
اما وقتی برای خراب کردن سرزمین اسرائیل بیایی، خشم من افروخته خواهد شد. | 18 |
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
من با غیرت و غضب گفتهام که در آن روز در اسرائیل زلزلهٔ مهیبی رخ خواهد داد. | 19 |
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
و در حضور من تمام حیوانات و انسانها خواهند لرزید. صخرهها تکان خواهند خورد و حصارها فرو خواهند ریخت. | 20 |
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
من که خداوند یهوه هستم میگویم تو را ای جوج، به هر نوع ترسی گرفتار خواهم ساخت و سربازان تو به جان هم افتاده، یکدیگر را خواهند کشت! | 21 |
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
من با شمشیر، مرض، طوفانهای سهمگین و سیلآسا، تگرگ درشت و آتش و گوگرد با تو و با تمام سربازان و همپیمانانت خواهم جنگید. | 22 |
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
به این طریق عظمت و قدوسیت خویش را به همهٔ قومهای جهان نشان خواهم داد و آنها خواهند دانست که من یهوه هستم.» | 23 |
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’