< حِزِقیال 37 >

دست خداوند بر من قرار گرفت و مرا در روح خداوند به دره‌ای که پر از استخوانهای خشک بود، برد. 1
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
او مرا به هر سو در میان استخوانها که روی زمین پخش شده بودند گردانید. 2
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
سپس به من گفت: «ای پسر انسان، آیا این استخوانها می‌توانند دوباره جان بگیرند و انسانهای زنده‌ای شوند؟» گفتم: «ای خداوند یهوه، تو می‌دانی.» 3
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
آنگاه به من فرمود که بر این استخوانها نوبت کرده، بگویم: «ای استخوانهای خشک به کلام خداوند گوش دهید! 4
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
خداوند یهوه می‌گوید: من به شما جان می‌بخشم تا دوباره زنده شوید. 5
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
گوشت و پی به شما می‌دهم و با پوست، شما را می‌پوشانم. در شما روح می‌دمم تا زنده شوید. آنگاه خواهید دانست که من یهوه هستم.» 6
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
آنچه را که خداوند فرموده بود به استخوانها گفتم. ناگهان سروصدایی برخاست و استخوانهای هر بدن به یکدیگر پیوستند! 7
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
سپس در حالی که نگاه می‌کردم، دیدم گوشت و پی بر روی استخوانها ظاهر شد و پوست، آنها را پوشانید. اما بدنها هنوز جان نداشتند. 8
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
خداوند یهوه به من فرمود: «ای پسر انسان به روح بگو از چهار گوشهٔ دنیا بیاید و به بدنهای این کشته‌شدگان بدمد تا دوباره زنده شوند.» 9
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
پس همان‌طور که خداوند به من امر فرموده بود گفتم و روح داخل بدنها شد و آنها زنده شده، ایستادند و لشکری بزرگ تشکیل دادند. 10
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
سپس خداوند معنی این رؤیا را به من فرمود: «این استخوانها قوم اسرائیل هستند؛ آنها می‌گویند:”ما به صورت استخوانهای خشک شده در آمده‌ایم و همهٔ امیدهایمان بر باد رفته است.“ 11
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
ولی تو به ایشان بگو که خداوند یهوه می‌فرماید: ای قوم من اسرائیل، من قبرهای اسارت شما را که در آنها دفن شده‌اید می‌گشایم و دوباره شما را زنده می‌کنم و به سرزمین اسرائیل باز می‌گردانم. 12
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
سرانجام، ای قوم من، خواهید دانست که من یهوه هستم. 13
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
روح خود را در شما قرار می‌دهم و شما بار دیگر احیا شده، به وطن خودتان باز می‌گردید. آنگاه خواهید دانست من که یهوه هستم به قولی که داده‌ام عمل می‌کنم.» 14
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
این پیغام نیز از طرف خداوند بر من نازل شد: 15
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«یک عصا بگیر و روی آن این کلمات را بنویس:”برای یهودا و اسرائیلیانِ متحد با او“. بعد یک عصای دیگر بگیر و این کلمات را روی آن بنویس:”برای یوسف (یعنی افرایم) و تمامی خاندان اسرائیل که با او متحدند“. 16
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
هر دو آنها را به هم بچسبان تا مثل یک عصا در دستت باشند. 17
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
وقتی قومت بپرسند که منظورت از اینها چیست، 18
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
به آنها بگو:”خداوند یهوه چنین می‌فرماید: من افرایم و قبایل اسرائیل را به یهودا ملحق می‌سازم و آنها مثل یک عصا در دستم خواهند بود.“ 19
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
پس در حالی که آن عصاها را که روی آنها نوشتی، دراز می‌کنی تا مردم ببینند 20
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
به ایشان بگو که خداوند یهوه می‌فرماید: قوم اسرائیل را از میان قومها جمع می‌کنم و از سراسر دنیا ایشان را به وطن خودشان باز می‌گردانم 21
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
تا به صورت یک قوم واحد درآیند. یک پادشاه بر همهٔ ایشان سلطنت خواهد کرد. دیگر به دو قوم تقسیم نخواهند شد، 22
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
و دیگر با بت‌پرستی و سایر گناهان، خودشان را آلوده نخواهند ساخت. من ایشان را از همهٔ گناهانشان پاک می‌سازم و نجات می‌دهم. آنگاه قوم واقعی من خواهند شد و من خدای ایشان خواهم بود. 23
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
خدمتگزار من داوود، پادشاه ایشان خواهد شد و آنها یک رهبر خواهند داشت و تمام دستورها و قوانین مرا اطاعت نموده، خواسته‌هایم را بجا خواهند آورد. 24
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
آنها در سرزمینی که پدرانشان زندگی کردند، ساکن می‌شوند، یعنی همان سرزمینی که به خدمتگزارم یعقوب دادم. خود و فرزندان و نوه‌هایشان، نسل اندر نسل، در آنجا ساکن خواهند شد. خدمتگزارم داوود تا به ابد پادشاه آنان خواهد بود. 25
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
من با ایشان عهد می‌بندم که تا به ابد ایشان را در امنیت نگه دارم. من آنها را در سرزمینشان مستقر کرده، جمعیت‌شان را زیاد خواهم نمود و خانهٔ مقدّس خود را تا به ابد در میان ایشان قرار خواهم داد. 26
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
خانهٔ من در میان ایشان خواهد بود و من خدای ایشان خواهم بود و آنها قوم من. 27
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
وقتی خانهٔ مقدّس من تا ابد در میان ایشان برقرار بماند، آنگاه سایر قومها خواهند دانست من که یهوه هستم قوم اسرائیل را برای خود انتخاب کرده‌ام.» 28
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< حِزِقیال 37 >