< حِزِقیال 28 >

پیغام دیگری از جانب خداوند به من داده شد: 1
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان، به حاکم صور بگو که خداوند یهوه می‌فرماید: تو به قدری مغرور شده‌ای که فکر می‌کنی خدا هستی و در قلمرو خود که جزیره‌ای است در وسط دریا، مانند یک خدا بر تخت نشسته‌ای! هر چند به خود می‌بالی که مثل خدا هستی، ولی بدان که انسانی بیش نیستی. تو می‌گویی از دانیال داناتری و هیچ رازی از تو مخفی نیست. 2
“Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
3
Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
با حکمت و دانایی خود، مال و ثروت زیاد جمع کرده‌ای و طلا و نقره و گنجهای بسیار اندوخته‌ای. 4
Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
حکمت تو، تو را بسیار ثروتمند و مغرور کرده است. 5
Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
«پس خداوند یهوه می‌فرماید: چون ادعا می‌کنی که مانند خدا دانا هستی، 6
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
من سپاه دشمن بی‌رحمی را که مایهٔ وحشت قومهاست می‌فرستم تا شکوه و زیبایی تو را که به حکمت خود به دست آورده‌ای از بین ببرند. 7
zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
آنها تو را به قعر جهنم می‌فرستند و تو در قلب دریا خواهی مرد. 8
Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
آیا در حضور قاتلان خود باز ادعای خدایی خواهی کرد؟ نه، بلکه در آن هنگام تو یک انسان خواهی بود و نه خدا. 9
Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
مثل یک شخص مطرود، به دست بیگانه‌ها کشته خواهی شد. من که خداوند یهوه هستم این را گفته‌ام.» 10
Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
بار دیگر خداوند به من فرمود: 11
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان، برای پادشاه صور گریه کن. به او بگو که خداوند یهوه می‌فرماید: تو مظهر کمال حکمت و زیبایی بودی 12
“Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
و در عدن که باغ خدا بود، قرار داشتی. خود را با انواع سنگهای گرانبها از قبیل عقیق سرخ، یاقوت زرد، الماس، زبرجد، جزع، یشم، یاقوت کبود، یاقوت سرخ و زمرد تزیین می‌کردی. زیورهای تو همه از طلا بود. تمام اینها در آن روزی که به وجود آمدی به تو داده شد. 13
Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
تو را به عنوان فرشتهٔ نگهبان انتخاب کردم. تو در کوه مقدّس من بودی و در میان سنگهای درخشان راه می‌رفتی. 14
An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
«از روزی که آفریده شدی در تمام کارهایت کامل و بی‌نقص بودی تا اینکه شرارت در تو راه یافت. 15
Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
تجارت زیاد تو با دیگران باعث شد تو ظالم و گناهکار شوی. به این سبب تو را از کوه خود بیرون انداختم. ای فرشتهٔ نگهبان، من تو را از میان سنگهای درخشان بیرون انداخته، هلاک ساختم. 16
Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
دل تو از زیبایی‌ات مغرور شد، و شکوه جلالت باعث شد حکمتت به حماقت تبدیل شود. به همین علّت تو را بر زمین انداختم و در برابر چشمان پادشاهان، درمانده‌ات کردم. 17
Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
تقدس خود را به سبب حرص و طمع از دست دادی. پس، از میان خودت آتشی بیرون آوردم و پیش چشمان کسانی که تماشا می‌کردند، تو را سوزاندم و به خاک و خاکستر تبدیل نمودم. 18
Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
تمام کسانی که تو را می‌شناختند، از آنچه که بر سرت آمده است حیران و وحشتزده شده‌اند. تو برای همیشه از بین رفته‌ای.» 19
Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
پیغامی دیگر از جانب خداوند به من رسید: 20
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان، به سوی شهر صیدون نگاه کرده، بر ضد آن پیشگویی کن و بگو 21
“Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
خداوند یهوه چنین می‌فرماید: «ای صیدون، من دشمن تو هستم و قدرتم را به تو نشان خواهم داد. وقتی با مجازات کردن تو قدوسیت خود را آشکار کنم، آنگاه خواهند دانست که من یهوه هستم. 22
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
امراض مسری بر تو می‌فرستم و سربازان دشمن از هر طرف به تو حمله کرده، ساکنان تو را از دم شمشیر خواهند گذراند و خون در کوچه‌هایت جاری خواهد شد. آنگاه خواهی دانست که من یهوه هستم. 23
Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
تو و سایر همسایگان اسرائیل، دیگر مثل خار، قوم اسرائیل را زخمی نخواهید کرد، هر چند که قبلاً آنها را خوار شمردید و با ایشان بدرفتاری کردید. 24
“‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
«خداوند یهوه می‌فرماید: قوم اسرائیل بار دیگر در سرزمین خود ساکن خواهند شد؛ بله، در سرزمینی که به پدرشان یعقوب دادم. زیرا ایشان را از سرزمینهای دور که آنها را در آنجا پراکنده ساخته‌ام برمی‌گردانم و بدین ترتیب به قومهای جهان نشان می‌دهم که من قدوس هستم. 25
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
قوم من با صلح و امنیت در سرزمین خود ساکن می‌شوند، برای خود خانه‌ها می‌سازند و تاکستانها غرس می‌کنند. وقتی همهٔ قومهای همسایه را به سبب رفتار توهین‌آمیزشان با قوم اسرائیل تنبیه کنم، آنگاه خواهند دانست که من یهوه خدای قوم اسرائیل هستم.» 26
Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”

< حِزِقیال 28 >