< خروج 8 >
خداوند به موسی فرمود: «پیش فرعون برگرد و به او بگو که خداوند چنین میفرماید: بگذار قوم من بروند و مرا عبادت کنند؛ | 1 |
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
و گرنه سرزمینت را پر از قورباغه خواهم نمود. | 2 |
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
رود نیل پر از قورباغه خواهد شد. قورباغهها از رود بیرون آمده، به کاخ تو هجوم خواهند آورد و حتی وارد خوابگاه و بسترت خواهند شد! نیز به خانههای درباریان و تمام قوم تو رخنه خواهند کرد. آنها حتی تغارهای خمیر و تنورهای نانوایی را پر خواهند ساخت. | 3 |
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
قورباغهها از سر و روی تو و مردم و درباریانت بالا خواهند رفت.» | 4 |
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
سپس خداوند به موسی فرمود: «به هارون بگو که عصای خود را به سوی رودخانهها، چشمهها و حوضها دراز کند تا قورباغهها بیرون بیایند و همه جا را پر سازند.» | 5 |
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
پس هارون دستش را به سوی آبهای مصر دراز کرد و قورباغهها بیرون آمده، سرزمین مصر را پوشاندند. | 6 |
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
ولی جادوگران مصری هم با جادوی خود، همین کار را کردند و قورباغههای بسیار زیادی پدید آوردند. | 7 |
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
پس فرعون، موسی و هارون را فرا خواند و گفت: «از خداوند درخواست کنید این قورباغهها را از ما دور کند و من قول میدهم بنیاسرائیل را رها کنم تا بروند و برای خداوند قربانی کنند.» | 8 |
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
موسی در جواب فرعون گفت: «زمانی را معین کن تا برای تو و درباریان و قومت دعا کنم و تمام قورباغهها بهجز آنهایی که در رود نیل هستند نابود شوند.» | 9 |
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
فرعون گفت: «فردا.» موسی جواب داد: «این کار را خواهم کرد تا تو بدانی که هیچکس مانند خدای ما یهوه نیست. | 10 |
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
تمام قورباغهها از تو و خانهات، و از درباریان و قومت دور خواهند شد. آنها فقط در رود نیل باقی خواهند ماند.» | 11 |
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
موسی و هارون از دربار فرعون بیرون آمدند و موسی از خداوند خواهش کرد تا قورباغهها را از بین ببرد. | 12 |
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
خداوند هم دعای موسی را اجابت فرمود و تمام قورباغهها در سراسر مصر مردند. | 13 |
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
مردم آنها را جمع کرده، روی هم انباشتند، آنچنان که بوی تعفن همه جا را فرا گرفت. | 14 |
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
اما وقتی قورباغهها از بین رفتند، فرعون باز هم دل خود را سخت کرد و همانطور که خداوند فرموده بود راضی نشد قوم اسرائیل را رها کند. | 15 |
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
آنگاه خداوند به موسی فرمود: «به هارون بگو که عصای خود را به زمین بزند تا گرد و غبار در سراسر مصر به پشه تبدیل شود.» | 16 |
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
موسی و هارون همانطور که خداوند به ایشان فرموده بود عمل کردند. وقتی هارون عصای خود را به زمین زد انبوه پشه سراسر خاک مصر را فرا گرفت و پشهها بر مردم و حیوانات هجوم بردند. | 17 |
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
جادوگران مصر هم سعی کردند همین کار را بکنند، ولی این بار موفق نشدند. | 18 |
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
پس به فرعون گفتند: «دست خدا در این کار است.» ولی همانطور که خداوند فرموده بود، دل فرعون باز نرم نشد و به موسی و هارون اعتنایی نکرد. | 19 |
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
پس خداوند به موسی فرمود: «صبح زود برخیز و به کنار رودخانه برو و منتظر فرعون باش. وقتی او به آنجا آید به او بگو که خداوند میفرماید: قوم مرا رها کن تا بروند و مرا عبادت کنند، | 20 |
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
و گرنه خانهٔ تو و درباریان و تمام مردم مصر را از مگس پر میکنم و زمین از مگس پوشیده خواهد شد. | 21 |
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
اما در سرزمین جوشن که محل سکونت بنیاسرائیل است، مگسی نخواهد بود تا بدانی که من خداوند این سرزمین هستم | 22 |
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
و بین قوم تو و قوم خود فرق میگذارم. این معجزه فردا ظاهر خواهد شد.» | 23 |
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
خداوند به طوری که فرموده بود، قصر فرعون و خانههای درباریان را پر از مگس کرد و در سراسر خاک مصر ویرانی به بار آمد. | 24 |
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
پس فرعون، موسی و هارون را فراخواند و به آنها گفت: «بسیار خوب، به شما اجازه میدهم که برای خدای خود قربانی کنید، ولی از مصر بیرون نروید.» | 25 |
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
موسی جواب داد: «ما نمیتوانیم در برابر چشمان مصریها حیواناتی که آنها از کشتنشان کراهت دارند، برای خداوند، خدای خود قربانی کنیم؛ چون ممکن است ما را سنگسار کنند. | 26 |
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
ما باید با یک سفر سه روزه، از مصر دور شویم و طبق دستور خداوند، در صحرا برای خداوند، خدای خود قربانی کنیم.» | 27 |
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
فرعون گفت: «من به شما اجازه میدهم تا به صحرا بروید و برای خداوند، خدای خود قربانی تقدیم کنید؛ ولی زیاد دور نشوید. حال، برای من دعا کنید.» | 28 |
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
موسی گفت: «وقتی از اینجا خارج شوم، نزد خداوند دعا خواهم کرد و فردا این بلا از تو و درباریان و مردم مصر دور خواهد شد. اما مواظب باش بار دیگر ما را فریب ندهی، بلکه بگذاری قوم من برود و برای خداوند قربانی تقدیم کند.» | 29 |
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
پس موسی از حضور فرعون بیرون رفت و نزد خداوند دعا کرد. | 30 |
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
خداوند دعای موسی را اجابت فرمود و تمام مگسها را از فرعون و قومش دور کرد، به طوری که حتی یک مگس هم باقی نماند. | 31 |
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
ولی این بار نیز دل فرعون نرم نشد و اجازه نداد قوم اسرائیل از مصر بیرون بروند. | 32 |
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.