< خروج 3 >

روزی هنگامی که موسی مشغول چرانیدن گلهٔ پدرزن خود یَترون، کاهن مدیان بود، گله را به آن سوی بیابان، به طرف کوه حوریب، معروف به کوه خدا راند. 1
Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
ناگهان فرشتهٔ خداوند از درون بوته‌ای مشتعل بر او ظاهر شد. موسی دید که بوته شعله‌ور است، ولی نمی‌سوزد. 2
A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
با خود گفت: «عجیب است! چرا بوته نمی‌سوزد؟» پس نزدیک رفت تا علّتش را بفهمد. 3
Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
وقتی خداوند دید که موسی به بوته نزدیک می‌شود، از میان بوته ندا داد: «موسی! موسی!» موسی جواب داد: «بله، می‌شنوم!» 4
Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
خدا فرمود: «بیش از این نزدیک نشو! کفشهایت را درآور، زیرا جایی که بر آن ایستاده‌ای، زمین مقدّس است. 5
Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
من هستم خدای اجدادت، خدای ابراهیم، خدای اسحاق و خدای یعقوب.» موسی روی خود را پوشاند، چون ترسید به خدا نگاه کند. 6
Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
خداوند فرمود: «من رنج و مصیبت قوم خود را در مصر دیده‌ام و ناله‌هایشان را برای رهایی از بردگی شنیده‌ام. بله، من از رنجشان آگاهم. 7
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
اکنون نزول کرده‌ام تا آنها را از چنگ مصری‌ها آزاد کنم و ایشان را از مصر بیرون آورده، به سرزمین خوب و پهناوری که در آن شیر و عسل جاری است ببرم، سرزمینی که اینک قبایل کنعانی، حیتّی، اموری، فرزّی، حوّی و یبوسی در آن زندگی می‌کنند. 8
Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
آری، ناله‌های بنی‌اسرائیل به گوش من رسیده است و ظلمی که مصری‌ها به ایشان می‌کنند، از نظر من پنهان نیست. 9
Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
حال، تو را نزد فرعون می‌فرستم تا قوم من بنی‌اسرائیل را از مصر بیرون آوری.» 10
To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
موسی گفت: «خدایا، من کیستم که نزد فرعون بروم و بنی‌اسرائیل را از مصر بیرون آورم؟» 11
Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
خدا فرمود: «من با تو خواهم بود و وقتی بنی‌اسرائیل را از مصر بیرون آوردی، در همین کوه مرا عبادت خواهید کرد. این نشانه‌ای خواهد بود که من تو را فرستاده‌ام.» 12
Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
موسی عرض کرد: «اگر نزد بنی‌اسرائیل بروم و به ایشان بگویم که خدای اجدادشان، مرا برای نجات ایشان فرستاده است، و آنها از من بپرسند:”نام او چیست؟“به آنها چه جواب دهم؟» 13
Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
خدا فرمود: «هستم آنکه هستم! به ایشان بگو”هستم“مرا نزد شما فرستاده است.» 14
Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
و باز خدا به موسی گفت: «به بنی‌اسرائیل بگو:”یهوه، خدای اجداد شما، خدای ابراهیم، خدای اسحاق و خدای یعقوب مرا نزد شما فرستاده است.“«این نام جاودانهٔ من است و تمام نسلها مرا به این نام خواهند شناخت. 15
Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
«حال، برو و تمام مشایخ اسرائیل را جمع کن و به ایشان بگو:”یهوه، خدای اجداد شما، خدای ابراهیم، اسحاق و یعقوب بر من ظاهر شد و فرمود: من از نزدیک مشاهده کرده و دیده‌ام چگونه مصری‌ها با شما رفتار کرده‌اند. 16
“Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
من وعده داده‌ام که شما را از سختیهایی که در مصر می‌کشید، آزاد کنم و به سرزمینی ببرم که در آن شیر و عسل جاری است، سرزمینی که اینک کنعانی‌ها، حیتی‌ها، اموری‌ها، فرزی‌ها، حوی‌ها و یبوسی‌ها در آن زندگی می‌کنند.“ 17
Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
«مشایخ اسرائیل سخن تو را خواهند پذیرفت. تو همراه آنان به حضور پادشاه مصر برو و به او بگو:”یهوه، خدای عبرانی‌ها، از ما دیدار کرده است. اجازه بده به فاصلهٔ سه روز راه، به صحرا برویم و در آنجا به یهوه، خدای خود قربانی تقدیم کنیم.“ 18
“Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
«ولی من می‌دانم که پادشاه مصر اجازه نخواهد داد که بروید، مگر آن که دستی نیرومند او را مجبور سازد. 19
Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
پس من دست خود را بلند کرده، مصری‌ها را با انجام همه نوع معجزات در میانشان خواهم زد. پس از آن او شما را رها خواهد کرد. 20
Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
من کاری می‌کنم که مصری‌ها برای شما احترام قائل شوند، به طوری که وقتی آن سرزمین را ترک می‌گویید، تهیدست نخواهید رفت. 21
“Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
هر زن اسرائیلی از همسایۀ مصری خود و از بانوی میهمان در خانه‌اش اجناسی از نقره و طلا و لباس خواهد خواست. شما آنها را بر پسران و دخترانتان خواهید پوشاند. به این ترتیب شما مصری‌ها را غارت خواهید کرد.» 22
Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”

< خروج 3 >