< خروج 12 >

خداوند در سرزمین مصر به موسی و هارون فرمود: 1
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
«از این پس باید این ماه برای شما اولین و مهمترین ماه سال باشد. 2
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
پس به تمام قوم اسرائیل بگویید که هر سال در روز دهم همین ماه، هر خانواده‌ای از ایشان یک بره یا یک بزغاله تهیه کند. طوری که یک حیوان برای یک خانواده باشد. 3
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
اگر تعداد افراد خانواده‌ای کم باشد می‌تواند با خانوادهٔ کوچکی در همسایگی خود شریک شود، یعنی هر خانواده به تعداد افرادش به همان مقداری که خوراکش می‌باشد، سهم قیمت بره را بپردازد. 4
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
این حیوان، خواه گوسفند و خواه بز، باید نر و یک ساله و بی‌عیب باشد. 5
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
«از این حیوان خاص تا عصر روز چهاردهم این ماه خوب مراقبت کنید. سپس همهٔ قوم اسرائیل بره‌های خود را ذبح کنند. 6
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
و خون آنها را روی تیرهای عمودی دو طرف در و سر در خانه‌هایشان که در آن گوشت بره را می‌خورند، بپاشند. 7
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
در همان شب، گوشت را بریان کنند و با نان فطیر (نان بدون خمیرمایه) و سبزیهای تلخ بخورند. 8
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
گوشت را نباید خام یا آب‌پز بخورند، بلکه همه را بریان کنند حتی کله و پاچه و دل و جگر آن را. 9
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
تمام گوشت باید تا صبح خورده شود، و اگر چیزی از آن باقی ماند آن را بسوزانند. 10
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
«قبل از خوردن بره، کفش به پا کنید، چوبدستی به دست گیرید و خود را برای سفر آماده کنید، و بره را با عجله بخورید. این آیین، پِسَح خداوند خوانده خواهد شد. 11
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
چون من که خداوند هستم، امشب از سرزمین مصر گذر خواهم کرد و تمام پسران نخست‌زادۀ مصری‌ها و همهٔ نخست‌زاده‌های حیوانات ایشان را هلاک خواهم نمود و خدایان آنها را مجازات خواهم کرد. 12
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
خونی که شما روی تیرهای در خانه‌های خود می‌پاشید، نشانه‌ای بر خانه‌هایتان خواهد بود. من وقتی خون را ببینم از شما خواهم گذشت و فقط مصری‌ها را هلاک می‌کنم. 13
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
«هر سال به یادبود این واقعه برای خداوند جشن بگیرید. این آیین تا ابد برای تمام نسلهای آینده خواهد بود. 14
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
در این جشن که هفت روز طول می‌کشد باید فقط نان فطیر بخورید. در روز اول، خمیرمایه را از خانهٔ خود بیرون ببرید، زیرا اگر کسی در مدت این هفت روز نان خمیرمایه‌دار بخورد از میان قوم اسرائیل منقطع خواهد شد. 15
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
در روز اول و هفتم این جشن، باید تمام قوم به طور دسته جمعی خدا را عبادت کنند. در این دو روز به‌جز تهیهٔ خوراک کار دیگری نکنید. 16
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
«این عید که همراه نان فطیر جشن گرفته می‌شود، به شما یادآوری خواهد کرد که من در چنین روزی شما را از مصر بیرون آوردم. پس برگزاری این جشن بر شما و نسلهای آیندهٔ شما تا به ابد واجب خواهد بود. 17
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
از غروب روز چهاردهم تا غروب روز بیست و یکم این ماه باید نان بدون خمیرمایه بخورید. 18
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
در این هفت روز نباید اثری از خمیرمایه در خانه‌های شما باشد. در این مدت اگر کسی نان خمیرمایه‌دار بخورد، باید از میان قوم اسرائیل منقطع شود. رعایت این قوانین حتی برای غریبه‌ها نیز که در میان شما ساکن هستند واجب خواهد بود. 19
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
باز تأکید می‌کنم که در این هفت روز نان خمیرمایه‌دار نخورید. فقط نان فطیر بخورید.» 20
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
آنگاه موسی، مشایخ قوم را نزد خود خواند و به ایشان گفت: «بروید و بره‌هایی برای خانواده‌هایتان بگیرید و برای عید پِسَح آنها را قربانی کنید. 21
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
خون بره را در یک تشت بریزید و بعد با گیاه زوفا خون را روی تیرهای دو طرف در و سر در خانه‌هایتان بپاشید. هیچ‌کدام از شما نباید در آن شب از خانه بیرون رود. 22
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
آن شب خداوند از سرزمین مصر عبور خواهد کرد تا مصری‌ها را بکشد. ولی وقتی خون را روی تیرهای دو طرف در و سر در خانه‌هایتان ببیند از آنجا می‌گذرد و به”هلاک کننده“اجازه نمی‌دهد که وارد خانه‌هایتان شده، شما را بکشد. 23
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
برگزاری این مراسم برای شما و فرزندانتان یک فریضۀ ابدی خواهد بود. 24
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
وقتی به آن سرزمینی که خداوند وعدهٔ آن را به شما داده، وارد شدید، عید پِسَح را جشن بگیرید. 25
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
هرگاه فرزندانتان مناسبت این جشن را از شما بپرسند، 26
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
بگویید: عید پِسَح را برای خداوند به مناسبت آن شبی جشن می‌گیریم که او از مصر عبور کرده، مصری‌ها را کشت، ولی وقتی به خانه‌های ما اسرائیلی‌ها رسید از آنها گذشت و به ما آسیبی نرساند.» قوم اسرائیل روی بر خاک نهاده، خداوند را سجده نمودند. 27
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
سپس همان‌طور که خداوند به موسی و هارون دستور داده بود، عمل کردند. 28
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
نیمه‌شب، خداوند تمام پسران نخست‌زادۀ مصر را کشت، از پسر فرعون که جانشین او بود گرفته تا پسر غلامی که در سیاهچال زندانی بود. او حتی تمام نخست‌زاده‌های حیوانات ایشان را نیز از بین برد. 29
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
در آن شب فرعون و درباریان و تمام اهالی مصر از خواب بیدار شدند و ناله سر دادند، به طوری که صدای ناله و شیون آنها در سراسر مصر پیچید، زیرا خانه‌ای نبود که در آن کسی نمرده باشد. 30
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
فرعون در همان شب موسی و هارون را فرا خواند و به ایشان گفت: «هر چه زودتر از سرزمین مصر بیرون بروید و بنی‌اسرائیل را هم با خود ببرید. بروید و همان‌طور که خواستید خداوند را عبادت کنید. 31
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
گله‌ها و رمه‌های خود را هم ببرید. ولی پیش از اینکه بروید برای من نیز دعا کنید.» 32
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
اهالی مصر نیز به قوم اسرائیل اصرار می‌کردند تا هر چه زودتر از مصر بیرون بروند. آنها به بنی‌اسرائیل می‌گفتند: «تا همهٔ ما را به کشتن نداده‌اید از اینجا بیرون بروید.» 33
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
پس قوم اسرائیل تغارهای پر از خمیر بی‌مایه را درون پارچه پیچیدند و بر دوش خود بستند، 34
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
و همان‌طور که موسی به ایشان گفته بود از همسایه‌های مصری خود لباس و طلا و نقره خواستند. 35
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
خداوند بنی‌اسرائیل را در نظر اهالی مصر محترم ساخته بود، به طوری که هر چه از آنها خواستند به ایشان دادند. به این ترتیب آنها ثروت مصر را با خود بردند. 36
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
در همان شب بنی‌اسرائیل از رَمِسیس کوچ کرده، روانهٔ سوکوت شدند. تعداد ایشان به غیر از زنان و کودکان قریب به ششصد هزار مرد بود که پیاده در حرکت بودند. از قومهای دیگر نیز در میان آنها بودند که همراه ایشان از مصر بیرون آمدند. گله‌ها و رمه‌های فراوانی هم به همراه ایشان خارج شدند. 37
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
وقتی سر راه برای غذا خوردن توقف کردند، از همان خمیر فطیر که آورده بودند، نان پختند. از این جهت خمیر را با خود آورده بودند چون با شتاب از مصر بیرون آمدند و فرصتی برای پختن نان نداشتند. 39
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
بنی‌اسرائیل مدت چهارصد و سی سال در مصر زندگی کرده بودند. 40
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
در آخرین روز چهارصد و سی‌امین سال بود که لشکریان خداوند از سرزمین مصر بیرون آمدند. 41
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
خداوند آن شب را برای رهایی آنها از سرزمین مصر در نظر گرفته بود و قوم اسرائیل می‌بایست نسل اندر نسل، همه ساله در آن شب به یاد رهایی خود از دست مصری‌ها، برای خداوند جشن بگیرند. 42
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
آنگاه خداوند به موسی و هارون مقررات آیین پِسَح را چنین تعلیم داد: «هیچ بیگانه‌ای نباید از گوشت برهٔ پِسَح بخورد. 43
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
اما غلامی که خریداری و ختنه شده باشد می‌تواند از آن بخورد. 44
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
خدمتکار و میهمان غیریهودی نباید از آن بخورند. 45
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
تمام گوشت بره را در همان خانه‌ای که در آن نشسته‌اید بخورید. آن گوشت را از خانه نباید بیرون ببرید. هیچ‌یک از استخوانهای آن را نشکنید. 46
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
تمام قوم اسرائیل باید این مراسم را برگزار نمایند. 47
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
«اگر غریبه‌هایی در میان شما زندگی می‌کنند و مایلند این آیین را برای خداوند نگاه دارند، باید مردان و پسران ایشان ختنه شوند تا اجازه داشته باشند مثل شما در این آیین شرکت کنند. اما شخص ختنه نشده هرگز نباید از گوشت برهٔ قربانی بخورد. 48
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
تمام مقررات این جشن شامل حال غریبه‌هایی نیز که ختنه شده‌اند و در میان شما ساکنند، می‌شود.» 49
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
قوم اسرائیل تمام دستورها خداوند را که توسط موسی و هارون به ایشان داده شده بود، به کار بستند. 50
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
در همان روز خداوند تمام بنی‌اسرائیل را از مصر بیرون آورد. 51
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< خروج 12 >