< تثنیه 20 >

زمانی که به جنگ می‌روید و در برابر خود لشکری نیرومندتر از خود با اسبها و ارابه‌های جنگی زیاد می‌بینید، وحشت نکنید. خداوند، خدایتان با شماست، همان خدایی که شما را از مصر بیرون آورد. 1
Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
قبل از شروع جنگ، کاهنی در برابر لشکر اسرائیل بایستد و بگوید: 2
Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
«ای مردان اسرائیلی به من گوش کنید! امروز که به جنگ می‌روید از دشمن نترسید و جرأت خود را از دست ندهید؛ 3
Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
چون خداوند، خدایتان همراه شماست. او برای شما با دشمنانتان می‌جنگد و به شما پیروزی می‌بخشد.» 4
Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
آنگاه سرداران سپاه باید سربازان را خطاب کرده، چنین بگویند: «آیا در اینجا کسی هست که به تازگی خانه‌ای ساخته، ولی هنوز از آن استفاده نکرده باشد؟ اگر چنین کسی هست به خانه برگردد، چون ممکن است در این جنگ کشته شود و شخص دیگری از آن استفاده کند. 5
Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
آیا کسی هست که به تازگی تاکستانی غرس کرده، ولی هنوز میوه‌ای از آن نخورده باشد؟ اگر چنین کسی هست به خانه بازگردد، چون ممکن است در این جنگ کشته شود و شخص دیگری میوهٔ آن را بخورد. 6
Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
آیا کسی به تازگی دختری را نامزد کرده است؟ اگر چنین کسی هست به خانهٔ خود بازگردد و با نامزدش ازدواج کند، چون ممکن است در این جنگ بمیرد و شخص دیگری نامزد او را به زنی بگیرد.» 7
Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
سپس سرداران بگویند: «آیا در اینجا کسی هست که می‌ترسد و دلشوره دارد؟ اگر چنین کسی هست به خانه بازگردد تا روحیهٔ دیگران را تضعیف نکند.» 8
Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
پس از نطق سرداران، فرماندهانی برای سپاه تعیین شوند. 9
Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
هنگامی که به شهری نزدیک می‌شوید تا با آن بجنگید، نخست به مردم آنجا فرصت دهید خود را تسلیم کنند. 10
Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
اگر آنها دروازه‌های شهر را به روی شما باز کردند، وارد شهر بشوید و مردم آنجا را اسیر کرده، به خدمت خود بگیرید؛ 11
In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
ولی اگر تسلیم نشدند، شهر را محاصره کنید. 12
In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
هنگامی که خداوند، خدایتان آن شهر را به شما داد، همهٔ مردانِ آن را از بین ببرید؛ 13
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
ولی زنها و بچه‌ها، گاوها و گوسفندها، و هر چه را که در شهر باشد می‌توانید برای خود نگه دارید. تمام غنایمی را که از دشمن به دست می‌آورید مال شماست. خداوند آنها را به شما داده است. 14
Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
این دستورها فقط شامل شهرهای دور دست می‌باشند و نه شهرهایی که در خود سرزمین موعود هستند. 15
Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
در شهرهای داخل مرزهای سرزمین موعود، هیچ‌کس را نباید زنده بگذارید. هر موجود زنده‌ای را از بین ببرید. 16
Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
حیتی‌ها، اموری‌ها، کنعانی‌ها، فرزی‌ها، حوی‌ها و یبوسی‌ها را به کلی نابود کنید. این حکمی است که خداوند، خدایتان داده است. 17
Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
منظور از این فرمان آن است که نگذارد مردم این سرزمین، شما را فریب داده، در دام بت‌پرستی و آداب و رسوم قبیح خود گرفتار سازند و شما را وادارند گناه بزرگی نسبت به خداوند، خدایتان مرتکب شوید. 18
In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
زمانی که شهری را برای مدت طولانی محاصره می‌کنید، درختان میوه را از بین نبرید. از میوهٔ آنها بخورید، ولی درختان را قطع نکنید. درختان، دشمنان شما نیستند! 19
Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
اما درختان دیگر را می‌توانید قطع کنید و از آنها برای محاصرهٔ شهر استفاده کنید. 20
Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.

< تثنیه 20 >