< تثنیه 13 >
اگر در میان شما پیشگو یا تعبیرکنندهٔ خواب وجود دارد که آینده را پیشگویی میکند | 1 |
In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
و پیشگوییهایش نیز درست از آب در میآیند، ولی میگوید: «بیایید تا خدایان قومهای دیگر را که شما نمیشناسید، بپرستیم» | 2 |
in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
به حرف او گوش نکنید؛ چون یهوه خدایتان بدین ترتیب شما را امتحان میکند تا معلوم شود آیا براستی او را با تمامی دل و جانتان دوست دارید یا نه. | 3 |
kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
فقط از خداوند، خدایتان پیروی کنید و او را احترام نمایید و اوامرش را به جا آورید، او را پرستش کنید و از او جدا مشوید. | 4 |
Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
آن پیشگو یا تعبیر کنندهٔ خواب را که سعی میکند شما را گمراه سازد، بکشید، چون قصد داشته شما را بر ضد خداوند، خدایتان که شما را از بردگی در مصر بیرون آورد، برانگیزد. با کشتن او شرارت را از میان خود پاک خواهید کرد. | 5 |
Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
اگر نزدیکترین خویشاوند یا صمیمیترین دوست شما، حتی برادر، پسر، دختر و یا همسرتان در گوش شما نجوا کند که «بیا برویم و این خدایان بیگانه را بپرستیم»، خدایانی که نه شما آنها را میشناسید و نه اجدادتان، | 6 |
In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
خدایان قومهایی که اطراف سرزمین شما هستند، خواه نزدیک به شما خواه دور، | 7 |
allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
به او گوش ندهید. پیشنهاد ناپسندش را برملا سازید و بر او رحم نکنید. | 8 |
kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
او را بکشید. دست خودتان باید اولین دستی باشد که او را سنگسار میکند و بعد دستهای تمامی قوم اسرائیل. | 9 |
Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
او را سنگسار کنید تا بمیرد، چون قصد داشته است شما را از خداوند، خدایتان که شما را از مصر یعنی سرزمین بردگی بیرون آورد دور کند. | 10 |
Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
آنگاه تمام بنیاسرائیل از کردار شرورانهاش آگاه شده، از ارتکاب چنین شرارتی در میان قوم خواهند ترسید. | 11 |
Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
هرگاه بشنوید در یکی از شهرهای اسرائیل میگویند که گروهی اوباش با پیشنهاد پرستیدن خدایان بیگانه همشهریان خود را گمراه کردهاند، اول حقایق را بررسی کنید و ببینید آیا آن شایعه حقیقت دارد یا نه. اگر دیدید حقیقت دارد و چنین عمل زشتی در میان شما در یکی از شهرهایی که یهوه خدایتان به شما داده است اتفاق افتاده، | 12 |
In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
باید بیدرنگ شهر و کلیهٔ ساکنانش را نابود کنید و گلههایشان را نیز از بین ببرید. | 15 |
dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
سپس باید تمام غنایم را در میدان شهر انباشته، بسوزانید. پس از آن، تمام شهر را به عنوان قربانی سوختنی برای خداوند، خدایتان به آتش بکشید. آن شهر برای همیشه باید ویرانه بماند و نباید هرگز دوباره آباد گردد. | 16 |
Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
ذرهای از این غنایم حرام را نگاه ندارید. آنگاه خداوند از غضب خود برمیگردد و شما را مورد لطف و مرحمت خویش قرار داده، همچنانکه با سوگند به پدرانتان وعده فرمود، تعداد شما را زیاد خواهد کرد، | 17 |
Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
به شرطی که فقط از یهوه خدایتان و فرمانهای او که امروز به شما میدهم اطاعت نموده، آنچه را که در نظر یهوه خدایتان پسندیده است بجا آورید. | 18 |
domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.