< دوم پادشاهان 1 >
بعد از مرگ اَخاب، پادشاه اسرائیل، قوم موآب علیه اسرائیل شورش کرد. | 1 |
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
در آن روزها اخزیا، پادشاه جدید اسرائیل از ایوان طبقهٔ بالای قصر خود در سامره به زیر افتاده، به شدت مجروح شده بود. وی قاصدانی به معبد بعلزبوب، بُت اهالی عقرون فرستاد تا بپرسند که آیا بهبود خواهد یافت یا نه. | 2 |
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
اما فرشتهٔ خداوند به ایلیای نبی دستور داد تا خود را به قاصدان پادشاه برساند و بگوید: «آیا در اسرائیل خدایی نیست که شما نزد بعلزبوب خدای عقرون میروید تا از او بپرسید که پادشاه بهبود مییابد یا نه؟ | 3 |
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
به پادشاه بگویید که خداوند میفرماید: چون چنین کاری کردهای از بستر بیماری برنخواهی خاست و خواهی مرد.» | 4 |
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
فرستادگان وقتی این خبر را از زبان ایلیا شنیدند نزد پادشاه بازگشتند. پادشاه از ایشان پرسید: «چرا به این زودی بازگشتید؟» | 5 |
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
گفتند: «در راه با شخصی روبرو شدیم و او به ما گفت تا نزد شما بازگردیم و بگوییم که خداوند میفرماید: چرا قاصدان میفرستی تا از بعلزبوب خدای عقرون سؤال کنند؟ مگر در اسرائیل خدایی وجود ندارد؟ حال که چنین کردهای، از بستر بیماری برنخواهی خاست و خواهی مرد.» | 6 |
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
پادشاه پرسید: «ظاهر این شخص چگونه بود؟» | 7 |
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
گفتند: «پوستینی بر تن داشت و کمربندی چرمی بر کمر بسته بود.» پادشاه گفت: «او همان ایلیای تِشبی است!» | 8 |
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
پس سرداری را با پنجاه سرباز مأمور کرد تا او را بیاورند. آنها او را در حالی که روی تپهای نشسته بود پیدا کردند. آن سردار به ایلیا گفت: «ای مرد خدا، پادشاه دستور داده است همراه ما بیایی.» | 9 |
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
ولی ایلیا جواب داد: «اگر من مرد خدا هستم، آتش از آسمان نازل شود و تو و پنجاه سربازت را نابود کند!» ناگهان آتش از آسمان نازل شد و آن سردار و سربازانش را کشت. | 10 |
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
پس پادشاه سردار دیگری را با پنجاه سرباز فرستاد تا به ایلیا بگوید: «ای مرد خدا، پادشاه دستور میدهد بیدرنگ پایین بیایی.» | 11 |
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
ایلیا جواب داد: «اگر من مرد خدا هستم آتش از آسمان نازل شود و تو و پنجاه سربازت را نابود کند!» بار دیگر آتش خدا از آسمان فرود آمد و آنها را نیز کشت. | 12 |
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
بار دیگر پادشاه پنجاه سرباز فرستاد، ولی این بار فرماندهٔ آنها در حضور ایلیا زانو زده، با التماس گفت: «ای مرد خدا، جان من و جان این پنجاه نفر خدمتگزارت را حفظ کن. | 13 |
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
ببین چطور آتش از آسمان آمد و دو گروه قبلی را نابود کرد. حال، تو جان مرا حفظ کن.» | 14 |
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
آنگاه فرشتهٔ خداوند به ایلیا گفت: «نترس! همراه او برو.» پس ایلیا همراه آن سردار نزد پادشاه رفت. | 15 |
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
ایلیا به پادشاه گفت: «خداوند میفرماید: چرا قاصدان نزد بعلزبوب خدای عقرون میفرستی تا دربارهٔ بهبودیت از او سؤال کنند؟ آیا به این دلیل چنین کردی که در اسرائیل خدایی نیست تا از او بپرسی؟ چون این کار را کردهای، از بستر بیماری برنخواهی خاست و خواهی مرد.» | 16 |
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
پس اخزیا درگذشت، همانطور که خداوند بهوسیلۀ ایلیا خبر داده بود؛ و چون پسری نداشت که جانشینش شود، برادرش یورام به جای او پادشاه شد. این واقعه در سال دوم سلطنت یهورام (پسر یهوشافاط) پادشاه یهودا اتفاق افتاد. | 17 |
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
شرح بقیهٔ رویدادهای سلطنت اخزیا و کارهای او در کتاب «تاریخ پادشاهان اسرائیل» ثبت شده است. | 18 |
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?