< دوم پادشاهان 24 >

در دورهٔ سلطنت یهویاقیم، نِبوکَدنِصَّر، پادشاه بابِل به اورشلیم حمله کرد. یهویاقیم تسلیم شد و سه سال به او باج و خراج پرداخت، اما بعد از آن، سر از فرمان وی پیچید و شورش نمود. 1
A zamani Yehohiyakim, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasar farmaki, Yehohiyakim dai ya zama abokin tarayyarsa na tsawon shekara uku. Daga baya kuma sai ya canja ra’ayi ya yi wa Nebukadnezzar tawaye.
خداوند لشکر بابِلی، سوری، موآبی و عمونی را فرستاد تا همان‌طور که به‌وسیلۀ انبیا خبر داده بود، یهودا را نابود کنند. 2
Ubangiji ya aiki maharan Babiloniyawa, da na Arameyawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa. Ya aike su su hallaka Yahuda bisa ga maganar Ubangiji wadda ya furta ta bakin bayinsa annabawa.
بدون شک این بلاها به فرمان خداوند بر یهودا نازل شد. خداوند تصمیم داشت یهودا را به سبب گناهان بی‌شمار مَنَسی طرد کند، 3
Ba shakka waɗannan abubuwa sun faru da Yahuda bisa ga umarnin Ubangiji domin yă kawar da su daga gabansa saboda zunuban Manasse da dukan abin da ya yi,
زیرا مَنَسی اورشلیم را از خون بی‌گناهان پر کرده بود و خداوند نخواست این گناهان را ببخشد. 4
haɗe da zub da jinin marasa laifi. Gama ya ƙazantar da Urushalima da jinin marasa laifi. Ubangiji kuwa bai yi niyyar yafewa ba.
شرح بقیهٔ رویدادهای دوران سلطنت یهویاقیم و کارهای او در کتاب تاریخ پادشاهان یهودا نوشته شده است. 5
Game da sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim da abubuwan da ya aikata, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
پس از مرگ یهویاقیم پسرش یهویاکین به جای او بر تخت سلطنت نشست. 6
Yehohiyakim ya huta da kakanninsa. Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi.
(پادشاه مصر دیگر از مرزهای خود خارج نشد، زیرا پادشاه بابِل تمام متصرفات مصر را که شامل یهودا هم می‌شد، از نهر مصر تا رود فرات، اشغال نمود.) 7
Sarkin Masar bai sāke fita daga ƙasarsa don yaƙi ba domin sarkin Babilon ya mamaye yankin, daga Rafin Masar har zuwa Kogin Yuferites.
یهویاکین هجده ساله بود که پادشاه یهودا شد و سه ماه در اورشلیم سلطنت کرد. (مادرش نحوشطا، دختر الناتان و از اهالی اورشلیم بود.) 8
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas da ya zama sarki, ya kuma yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Nehushta’yar Elnatan, mutuniyar Urushalima.
یهویاکین مانند پدرش نسبت به خداوند گناه ورزید. 9
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi.
در دورهٔ سلطنت یهویاکین، لشکر نِبوکَدنِصَّر، پادشاه بابِل، اورشلیم را محاصره کرد. 10
A wannan lokaci, hafsoshin Nebukadnezzar sarkin Babilon suka kawo wa Urushalima yaƙi, suka kuma kewaye ta.
وقتی شهر در محاصره بود، خود نِبوکَدنِصَّر هم به آنجا رسید. 11
Nebukadnezzar na Babilon da kansa kuwa ya zo birnin yayinda hafsoshinsa suka kewaye ta.
یهویاکین و تمام مقامات و فرماندهان و خدمتگزاران دربارش و ملکهٔ مادر تسلیم نِبوکَدنِصَّر شدند. پادشاه بابِل در سال هشتم سلطنت خود، یهویاکین را زندانی کرد. 12
Yehohiyacin sarkin Yahuda, da mahaifiyarsa, da masu yi masa hidima, da hakimansa, da kuma fadawansa duk suka miƙa kansu ga Nebukadnezzar. A shekara ta takwas ta mulkin sarkin Babilon, sarkin Babilon ya mai da Yehohiyacin ɗan kurkuku.
طبق آنچه خداوند فرموده بود، بابِلی‌ها تمام اشیاء قیمتی خانهٔ خداوند، جواهرات کاخ سلطنتی و تمام ظروف طلا را که سلیمان پادشاه برای خانهٔ خداوند ساخته بود، در هم شکستند. 13
Yadda Ubangiji ya faɗa, Nebukadnezzar ya kwashe dukan dukiyar haikalin Ubangiji, da ta fadan sarki, ya kuma kwashe dukan kayan zinariyar da Solomon sarkin Isra’ila ya ƙera domin haikalin Ubangiji.
نِبوکَدنِصَّر اهالی اورشلیم را که شامل فرماندهان و سربازان، صنعتگران و آهنگران می‌شدند و تعدادشان به ده هزار نفر می‌رسید به بابِل تبعید کرد، و فقط افراد فقیر را در آن سرزمین باقی گذاشت. 14
Ya kwashi dukan mutanen Urushalima zuwa bauta, ya kwashi dukan fadawa, da mayaƙa, da masu sana’a, da maƙera, yawansu ya kai dubu goma. Ba wanda ya ragu, sai matalautan ƙasar.
نِبوکَدنِصَّر، یهویاکین را با مادر و زنان او، فرماندهان و مقامات مملکتی به بابِل برد. 15
Nebukadnezzar ya ɗauki Yehohiyacin ya kai bauta a Babilon. Ya kuma kwashe mahaifiyar sarki, da matansa, da fadawansa, da manyan mutanen ƙasar daga Urushalima ya kai Babilon.
همچنین تمام سربازان جنگ آزموده را که هفت هزار نفر بودند و هزار صنعتگر و آهنگر را اسیر کرده، به بابِل برد. 16
Sarkin Babilon kuma ya kwashe dukan mayaƙa dubu bakwai, ƙarfafu, shiryayyu don yaƙi, da masu sana’a, da maƙera dubu ɗaya, ya kai Babilon.
بعد پادشاه بابِل متنیا عموی یهویاکین را به جای او به پادشاهی تعیین نمود و نامش را به صدقیا تغییر داد. 17
Sarkin Babilon ya sa Mattaniya, ɗan’uwan mahaifin Yehohiyacin, ya zama sarki a madadinsa, ya canja masa suna zuwa Zedekiya.
صدقیا بیست و یک ساله بود که پادشاه یهودا شد و یازده سال در اورشلیم سلطنت نمود. (مادرش حموطل، دختر ارمیا و از اهالی لبنه بود.) 18
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
او مانند یهویاقیم نسبت به خداوند گناه ورزید. 19
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Yehohiyakim ya yi.
خشم خداوند بر مردم اورشلیم و یهودا افروخته شد و او ایشان را طرد نمود. 20
Saboda fushin Ubangiji ne dukan waɗannan abubuwa suka faru da Urushalima, da kuma Yahuda, a ƙarshe kuma ya kawar da su daga fuskarsa. To, sai Zedekiya ya yi wa sarkin Babilon tawaye.

< دوم پادشاهان 24 >