< دوم تواریخ 21 >
وقتی یهوشافاط مرد، او را در آرامگاه سلطنتی در اورشلیم، شهر داوود، دفن کردند و پسر او یهورام به جای او به سلطنت رسید. | 1 |
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
برادران او، یعنی سایر پسران یهوشافاط، اینها بودند: عزریا، یحیئیل، زکریا، عزریاهو، میکائیل و شفطیا. | 2 |
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
پدرشان به هر یک از آنها هدایایی گرانبها از قبیل نقره و طلا و جواهرات و نیز شهرهای حصاردار در یهودا بخشیده بود. اما سلطنت را به یهورام داد چون پسر ارشدش بود. ولی یهورام وقتی زمام امور را به دست گرفت و بر اوضاع مسلط شد، تمام برادران خود و عدهٔ زیادی از بزرگان اسرائیل را کشت. | 3 |
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
یهورام در سن سی و دو سالگی پادشاه شد و هشت سال در اورشلیم سلطنت کرد، | 5 |
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
دختر اَخاب زن او بود و او مانند اَخاب و سایر پادشاهان اسرائیل نسبت به خداوند گناه میورزید. | 6 |
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
اما خداوند نخواست دودمان سلطنت داوود را براندازد، زیرا با داوود عهد بسته بود که همیشه یکی از پسرانش پادشاه باشد. | 7 |
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
در دورهٔ سلطنت یهورام، مردم ادوم از فرمان یهودا سرپیچی کردند و پادشاهی برای خود تعیین نمودند. | 8 |
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
یهورام و فرماندهان سپاه او با تمام ارابههای جنگی عازم ادوم شدند. اما ادومیها آنها را محاصره کردند و یهورام شبانه از دست ادومیها گریخت. | 9 |
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
به این ترتیب ادوم تا به امروز استقلال خود را از یهودا حفظ کرده است. در این هنگام اهالی شهر لبنه نیز شورش نمودند، زیرا یهورام از خداوند، خدای اجدادش برگشته بود. | 10 |
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
او همچنین بر بلندیهای یهودا بتخانهها ساخت و اهالی اورشلیم را به بتپرستی کشاند و باعث شد مردم یهودا از خدا دور شوند. | 11 |
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
یهورام نامهای از ایلیای نبی با این مضمون دریافت کرد: «خداوند، خدای جد تو داوود، میفرماید که چون مثل پدرت یهوشافاط و مانند آسا پادشاه یهودا رفتار نکردی، | 12 |
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
بلکه مثل پادشاهان اسرائیل شرور بودهای و مانند زمان اَخاب پادشاه، مردم یهودا و اورشلیم را به بتپرستی کشاندهای، و چون برادرانت را که از خودت بهتر بودند به قتل رساندی، | 13 |
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
پس خداوند بلای سختی دامنگیر قوم تو و زنان و فرزندانت خواهد کرد؛ و تو هر چه داری از دست خواهی داد. | 14 |
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
خودت نیز به مرض رودهای سختی مبتلا خواهی شد و این مرض آنقدر طول خواهد کشید تا رودههایت از بین برود.» | 15 |
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
بنابراین خداوند فلسطینیها و عربهایی را که همسایهٔ حبشیها بودند بر ضد یهورام برانگیخت. | 16 |
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
آنها به یهودا حمله کرده، آن را گرفتند و تمام اموال کاخ سلطنتی و پسران و زنان یهورام را برداشته، با خود بردند. فقط پسر کوچک او اخزیا جان به در برد. | 17 |
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
پس از آن، خداوند یهورام را به یک مرض علاجناپذیر رودهای مبتلا کرد. | 18 |
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
به مرور زمان، بعد از دو سال، رودههایش بیرون آمد و او با دردی جانکاه مرد. قومش مراسم مخصوص دفن پادشاهان را برای او انجام ندادند. | 19 |
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
یهورام سی و دو سال داشت که پادشاه شد و هشت سال در اورشلیم سلطنت کرد و هنگامی که مرد، کسی برایش عزا نگرفت. یهورام در شهر داوود دفن شد، اما نه در آرامگاه سلطنتی. | 20 |
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.