< اول سموئیل 12 >
سموئیل به مردم اسرائیل گفت: «هر چه از من خواستید برای شما انجام دادم. پادشاهی برای شما تعیین نمودم. | 1 |
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
حال، او شما را رهبری میکند. پسرانم نیز در خدمت شما هستند. ولی من پیر و سفید مو شدهام و از روزهای جوانیام تا به امروز در میان شما زندگی کردهام. | 2 |
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
اینک که در حضور خداوند و پادشاه برگزیدهٔ او ایستادهام، به من بگویید گاو و الاغ چه کسی را به زور گرفتهام؟ چه کسی را فریب دادهام و به که ظلم کردهام؟ از دست چه کسی رشوه گرفتهام تا حق را نادیده بگیرم؟ اگر چنین کردهام حاضرم جبران کنم.» | 3 |
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
همه در جواب وی گفتند: «تو هرگز کسی را فریب ندادهای، بر هیچکس ظلم نکردهای و رشوه نگرفتهای.» | 4 |
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
سموئیل گفت: «خداوند و پادشاه برگزیدهٔ او، امروز شاهدند که شما عیبی در من نیافتید.» مردم گفتند: «بله، همینطور است.» | 5 |
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
سموئیل گفت: «این خداوند بود که موسی و هارون را برگزید و اجداد شما را از مصر بیرون آورد. | 6 |
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
حال، در حضور خداوند بایستید تا کارهای شگفتانگیز خداوند را که در حق شما و اجدادتان انجام داده است به یاد شما آورم: | 7 |
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
«وقتی بنیاسرائیل در مصر بودند و برای رهایی خود به حضور خداوند فریاد برآوردند، خداوند موسی و هارون را فرستاد و ایشان بنیاسرائیل را به این سرزمین آوردند. | 8 |
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
اما بنیاسرائیل خداوند، خدای خود را از یاد بردند. پس خدا هم ایشان را به دست سیسرا سردار سپاه حاصور، فلسطینیها و پادشاه موآب سپرد و آنها با ایشان جنگیدند. | 9 |
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
آنها نزد خداوند فریاد برآورده، گفتند: ما گناه کردهایم، زیرا از پیروی تو برگشتهایم و بعل و عشتاروت را پرستیدهایم. حال، ما را از چنگ دشمنانمان برهان و ما فقط تو را پرستش خواهیم کرد. | 10 |
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
پس خداوند جدعون، باراق، یفتاح و سرانجام مرا فرستاد و شما را از دست دشمنان نجات داد تا شما در امنیت زندگی کنید. | 11 |
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
اما وقتی ناحاش، پادشاه بنیعمون را دیدید که قصد حمله به شما را دارد، نزد من آمدید و پادشاهی خواستید تا بر شما سلطنت کند و حال آنکه خداوند، خدایتان پادشاه شما بود. | 12 |
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
پس این است پادشاهی که شما برگزیدهاید. خود شما او را خواستهاید و خداوند هم خواست شما را اجابت نموده است. | 13 |
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
«حال اگر از خداوند بترسید و او را عبادت کرده، به کلامش گوش دهید و از فرمانش سرپیچی نکنید، و اگر شما و پادشاه شما خداوند، خدای خود را پیروی نمایید، همه چیز به خوبی پیش خواهد رفت؛ | 14 |
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
اما اگر برخلاف دستورهای خداوند، خدایتان رفتار کنید و به سخنان او گوش ندهید، آنگاه شما را مثل اجدادتان مجازات خواهد کرد. | 15 |
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
«حال، بایستید و این کار عظیم خداوند را مشاهده کنید. | 16 |
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
مگر نه اینکه در این فصل که گندم را درو میکنند از باران خبری نیست؟ ولی من دعا میکنم خداوند رعد و برق ایجاد کند و باران بباراند تا بدانید که کار خوبی نکردید که پادشاه خواستید چون با این کار، گناه بزرگی نسبت به خدا مرتکب شدید.» | 17 |
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
سپس، سموئیل در حضور خداوند دعا کرد و خداوند در همان روز رعد و برق و باران فرستاد و مردم از خداوند و از سموئیل بسیار ترسیدند. | 18 |
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
آنها به سموئیل گفتند: «در حضور خداوند، خدای خود برای ما دعا کن تا نمیریم؛ زیرا با خواستن پادشاه بار گناهان خود را سنگینتر کردیم.» | 19 |
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
سموئیل به آنها گفت: «نترسید! درست است که کار بدی کردهاید، ولی سعی کنید بعد از این با تمام وجود، خداوند را پرستش نمایید و به هیچ وجه از او روگردان نشوید. | 20 |
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
بتها را عبادت نکنید چون باطل و بیفایدهاند و نمیتوانند به داد شما برسند. | 21 |
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
خداوند به خاطر حرمت نام عظیم خود، هرگز قوم خود را ترک نخواهد کرد، زیرا خواست او این بوده است که شما را قوم خاص خود سازد. | 22 |
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
و اما من، محال است که از دعا کردن برای شما دست بکشم، و چنین گناهی نسبت به خداوند مرتکب شوم. من هر چه را که راست و نیکوست به شما تعلیم میدهم. | 23 |
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
شما باید تنها ترس خداوند را در دل داشته باشید و با وفاداری و از صمیم قلب او را عبادت نمایید و در کارهای شگفتانگیزی که برای شما انجام داده است تفکر کنید. | 24 |
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
اما اگر به گناه ادامه دهید، هم شما و هم پادشاهتان هلاک خواهید شد.» | 25 |
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.