< اول پادشاهان 15 >

در هجدهمین سال سلطنت یربعام، پادشاه اسرائیل، اَبیّام پادشاه یهودا شد و سه سال در اورشلیم سلطنت کرد. مادر او معکه دختر ابشالوم بود. 1
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
اَبیّام نیز مانند پدرش مرد فاسدی بود و مثل داوود پادشاه نبود که نسبت به خداوند وفادار باشد. 3
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
اما با وجود این، خداوند به خاطر نظر لطفی که به جد او داوود داشت، به اَبیّام پسری بخشید تا سلطنت خاندان داوود در اورشلیم برقرار بماند؛ 4
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
چون داوود در تمام عمر خود مطابق میل خداوند رفتار می‌نمود. او از دستورهای خداوند سرپیچی نکرد، به‌جز در مورد اوریای حیتی. 5
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
در طول سه سال سلطنت اَبیّام، بین رحُبعام و یربعام همیشه جنگ بود. 6
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
رویدادهای دیگر سلطنت اَبیّام در کتاب تاریخ پادشاهان یهودا نوشته شده است. میان اَبیّام و یربعام دائم جنگ بود. 7
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
وقتی اَبیّام مرد، او را در اورشلیم دفن کردند و پسرش آسا به جای او پادشاه شد. 8
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
در بیستمین سال سلطنت یربعام پادشاه اسرائیل، آسا پادشاه یهودا شد. 9
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
او چهل و یک سال در اورشلیم سلطنت کرد. مادر بزرگ او معکه دختر ابشالوم بود. 10
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
آسا هم مثل جد خود داوود، مطابق میل خداوند رفتار می‌کرد. 11
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
افرادی را که لواط می‌کردند از سرزمین خود اخراج کرد و تمام بتهایی را که پدرش بر پا کرده بود، در هم کوبید. 12
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
حتی مادر بزرگ خود معکه را به سبب اینکه بت می‌پرستید، از مقام ملکه‌ای برکنار کرد و بت او را شکست و در درهٔ قدرون سوزانید. 13
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
هر چند بتکده‌های بالای تپه‌ها به کلی از بین نرفت، اما آسا در تمام زندگی خویش نسبت به خداوند وفادار ماند. 14
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
آسا اشیاء طلا و نقره‌ای را که خود و پدرش وقف خانهٔ خداوند نموده بودند، در خانهٔ خداوند گذاشت. 15
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
آسا، پادشاه یهودا و بعشا، پادشاه اسرائیل همیشه با یکدیگر در حال جنگ بودند. 16
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
بعشا، پادشاه اسرائیل به یهودا لشکر کشید و شهر رامه را بنا کرد تا نگذارد کسی نزد آسا، پادشاه یهودا رفت و آمد کند. 17
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
آسا چون وضع را چنین دید، هر چه طلا و نقره در خزانه‌های خانۀ خداوند و کاخ سلطنتی بود گرفته، با این پیام برای بنهدد پسر طَبریمّون پسر حِزیون، پادشاه سوریه به دمشق فرستاد: 18
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
«بیا مثل پدرانمان با هم متحد شویم. این طلا و نقره را که برایت می‌فرستم از من بپذیر. پیوند دوستی خود را با بعشا، پادشاه اسرائیل قطع کن تا او از قلمرو من خارج شود.» 19
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
بنهدد موافقت کرد و با سپاهیان خود به اسرائیل حمله برد و شهرهای عیون، دان، آبل بیت‌معکه، ناحیهٔ دریاچهٔ جلیل و سراسر نفتالی را تسخیر کرد. 20
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
وقتی بعشا این را شنید، از ادامهٔ بنای رامه دست کشید و به ترصه بازگشت. 21
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
آنگاه آسا به سراسر یهودا پیغام فرستاد که همهٔ مردان بدون استثنا بیایند و سنگها و چوبهایی را که بعشا برای بنای رامه به کار می‌برد برداشته، ببرند. آسا با این مصالح، شهر جبع واقع در زمین بنیامین و شهر مصفه را بنا نهاد. 22
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
بقیهٔ رویدادهای سلطنت آسا، یعنی فتوحات و کارهای او و نام شهرهایی را که ساخته، همه در کتاب «تاریخ پادشاهان یهودا» نوشته شده است. آسا در سالهای پیری به پا درد سختی مبتلا شد. 23
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
وقتی آسا فوت کرد، او را در آرامگاه سلطنتی، در شهر پدرش داوود دفن کردند. بعد از او پسرش یهوشافاط به مقام پادشاهی یهودا رسید. 24
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
در سال دوم سلطنت آسا پادشاه یهودا، ناداب، پسر یربعام، پادشاه اسرائیل شد و دو سال سلطنت کرد. 25
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
او نیز مثل پدرش نسبت به خداوند گناه ورزید و اسرائیل را به گناه کشاند. 26
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
بعشا پسر اخیا از قبیلهٔ یساکار بر ضد ناداب برخاست و هنگامی که ناداب با سپاه خود شهر جبتون را که یکی از شهرهای فلسطین بود محاصره می‌کرد بعشا ناداب را کشت. 27
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
بعشا در سومین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا، به جای ناداب بر تخت سلطنت اسرائیل نشست. 28
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
او وقتی به قدرت رسید تمام فرزندان یربعام را کشت، به طوری که حتی یک نفر هم از خاندان او زنده نماند. این درست همان چیزی بود که خداوند به‌وسیلۀ خدمتگزارش اخیای شیلونی خبر داده بود؛ 29
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
زیرا یربعام نسبت به خداوند گناه ورزید و تمام اسرائیل را به گناه کشاند و خداوند، خدای قوم اسرائیل را خشمگین نمود. 30
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
جزئیات سلطنت ناداب در کتاب «تاریخ پادشاهان اسرائیل» نوشته شده است. 31
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
بین آسا، پادشاه یهودا و بعشا، پادشاه اسرائیل همیشه جنگ بود. 32
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
در سومین سال سلطنت آسا پادشاه یهودا، بعشا بر اسرائیل پادشاه شد و بیست و چهار سال در ترصه سلطنت کرد. 33
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
او نیز مثل یربعام نسبت به خداوند گناه ورزید و اسرائیل را به گناه کشاند. 34
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.

< اول پادشاهان 15 >