< مزامیر 86 >

دعای داود ای خداوند گوش خود را فراگرفته، مرامستجاب فرما زیرا مسکین و نیازمندهستم! ۱ 1
Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
جان مرا نگاه دار زیرا من متقی هستم. ای خدای من، بنده خود را که بر تو توکل دارد، نجات بده. ۲ 2
Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
‌ای خداوند بر من کرم فرما زیرا که تمامی روز تو را می‌خوانم! ۳ 3
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
جان بنده خود را شادمان گردان زیرا‌ای خداوند جان خود را نزد توبرمی دارم. ۴ 4
Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
زیرا تو‌ای خداوند، نیکو و غفارهستی و بسیار رحیم برای آنانی که تو رامی خوانند. ۵ 5
Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
‌ای خداوند دعای مرا اجابت فرما وبه آواز تضرع من توجه نما! ۶ 6
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
در روز تنگی خودتو را خواهم خواند زیرا که مرا مستجاب خواهی فرمود. ۷ 7
A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
‌ای خداوند در میان خدایان مثل تونیست و کاری مثل کارهای تو نی. ۸ 8
A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
‌ای خداوندهمه امت هایی که آفریده‌ای آمده، به حضور توسجده خواهند کرد و نام تو را تمجید خواهندنمود. ۹ 9
Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
زیرا که تو بزرگ هستی و کارهای عجیب می‌کنی. تو تنها خدا هستی. ۱۰ 10
Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
‌ای خداوند طریق خود را به من بیاموز تا درراستی تو سالک شوم. دل مرا واحد ساز تا از نام تو ترسان باشم. ۱۱ 11
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
‌ای خداوند خدای من تو را به تمامی دل حمد خواهم گفت و نام تو را تمجیدخواهم کرد تا ابدالاباد. ۱۲ 12
Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
زیرا که رحمت تو به من عظیم است و جان مرا از هاویه اسفل رهانیده‌ای. (Sheol h7585) ۱۳ 13
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
‌ای خدا متکبران بر من برخاسته اندو گروهی از ظالمان قصد جان من دارند و تو را در مد نظر خود نمی آورند. ۱۴ 14
Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
و تو‌ای خداوندخدای رحیم و کریم هستی. دیر غضب و پر ازرحمت و راستی. ۱۵ 15
Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
بسوی من التفات کن و بر من کرم فرما. قوت خود را به بنده ات بده و پسر کنیزخود را نجات‌بخش. ۱۶ 16
Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
علامت خوبی را به من بنما تا آنانی که از من نفرت دارند آن را دیده، خجل شوند زیرا که تو‌ای خداوند مرا اعانت کرده و تسلی داده‌ای. ۱۷ 17
Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.

< مزامیر 86 >