< مزامیر 74 >
قصیده آساف چراای خدا ما را ترک کردهای تا به ابدو خشم تو بر گوسفندان مرتع خودافروخته شده است؟ | ۱ 1 |
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
جماعت خود را که ازقدیم خریدهای، بیاد آور و آن را که فدیه دادهای تا سبط میراث تو شود و این کوه صهیون را که درآن ساکن بودهای. | ۲ 2 |
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
قدمهای خود را بسوی خرابه های ابدی بردار زیرا دشمن هرچه را که درقدس تو بود خراب کرده است. | ۳ 3 |
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
دشمنانت درمیان جماعت تو غرش میکنند و علمهای خودرا برای علامات برپا مینمایند. | ۴ 4 |
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
و ظاهرمی شوند چون کسانی که تبرها را بر درختان جنگل بلند میکنند. | ۵ 5 |
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
و الان همه نقشهای تراشیده آن را به تبرها و چکشها خرد میشکنند. | ۶ 6 |
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
قدس های تو را آتش زدهاند و مسکن نام تو را تابه زمین بیحرمت کردهاند. | ۷ 7 |
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
و در دل خودمی گویند آنها را تمام خراب میکنیم. پس جمیع کنیسه های خدا را در زمین سوزانیدهاند. | ۸ 8 |
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
آیات خود را نمی بینیم و دیگر هیچ نبی نیست. و درمیان ما کسی نیست که بداند تا به کی خواهد بود. | ۹ 9 |
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
ای خدا، دشمن تا به کی ملامت خواهد کرد؟ وآیا خصم، تا به ابد نام تو را اهانت خواهد نمود؟ | ۱۰ 10 |
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
چرا دست خود یعنی دست راست خویش رابرگردانیدهای؟ آن را از گریبان خود بیرون کشیده، ایشان را فانی کن. | ۱۱ 11 |
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
و خدا از قدیم پادشاه من است. او در میان زمین نجاتها پدید میآورد. | ۱۲ 12 |
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
تو به قوت خوددریا را منشق ساختی و سرهای نهنگان را در آبهاشکستی. | ۱۳ 13 |
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
سرهای لویاتان را کوفته، و او را خوراک صحرانشینان گردانیدهای. | ۱۴ 14 |
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
توچشمهها و سیلها را شکافتی و نهرهای دائمی راخشک گردانیدی. | ۱۵ 15 |
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
روز از آن توست و شب نیزاز آن تو. نور و آفتاب را تو برقرار نمودهای. | ۱۶ 16 |
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
تمامی حدود جهان را تو پایدار ساختهای. تابستان و زمستان را تو ایجاد کردهای. | ۱۷ 17 |
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
ای خداوند این را بیادآور که دشمن ملامت میکند و مردم جاهل نام تو را اهانت مینمایند. | ۱۸ 18 |
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
جان فاخته خود را بهجانور وحشی مسپار. جماعت مسکینان خود را تا به ابد فراموش مکن. | ۱۹ 19 |
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
عهد خود را ملاحظه فرما زیرا که ظلمات جهان از مسکن های ظلم پراست. | ۲۰ 20 |
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
مظلومان به رسوایی برنگردند. مساکین و فقیران نام تو را حمدگویند. | ۲۱ 21 |
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
ای خدا برخیز و دعوای خود را برپادار؛ و بیادآور که احمق تمامی روز تو را ملامت میکند. | ۲۲ 22 |
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
آواز دشمنان خود را فراموش مکن وغوغای مخالفان خود را که پیوسته بلند میشود. | ۲۳ 23 |
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.