< مزامیر 73 >
مزمور آساف هرآینه خدا برای اسرائیل نیکوست، یعنی برای آنانی که پاک دل هستند. | ۱ 1 |
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
واما من نزدیک بود که پایهایم از راه در رود ونزدیک بود که قدمهایم بلغزد. | ۲ 2 |
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
زیرا بر متکبران حسد بردم چون سلامتی شریران را دیدم. | ۳ 3 |
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
زیراکه در موت ایشان قیدها نیست و قوت ایشان مستحکم است. | ۴ 4 |
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
مثل مردم در زحمت نیستند ومثل آدمیان مبتلا نمی باشند. | ۵ 5 |
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
بنابراین گردن ایشان به تکبر آراسته است وظلم مثل لباس ایشان را میپوشاند. | ۶ 6 |
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
چشمان ایشان از فربهی بدرآمده است و از خیالات دل خود تجاوز میکنند. | ۷ 7 |
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
استهزا میکنند و حرفهای بد میزنند و سخنان ظلم آمیز را از جای بلندمی گویند. | ۸ 8 |
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
دهان خود را بر آسمانها گذاردهاند وزبان ایشان در جهان گردش میکند. | ۹ 9 |
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
پس قوم او بدینجا برمی گردند و آبهای فراوان، بدیشان نوشانیده میشود. | ۱۰ 10 |
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
و ایشان میگویند: «خدا چگونه بداند و آیا حضرت اعلی علم دارد؟» | ۱۱ 11 |
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
اینک اینان شریر هستند که همیشه مطمئن بوده، در دولتمندی افزوده میشوند. | ۱۲ 12 |
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
یقین من دل خود را عبث طاهر ساخته و دستهای خود رابه پاکی شستهام. | ۱۳ 13 |
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
و من تمامی روز مبتلامی شوم و تادیب من هر بامداد حاضر است. | ۱۴ 14 |
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
اگر میگفتم که چنین سخن گویم، هر آینه برطبقه فرزندان تو خیانت میکردم. | ۱۵ 15 |
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
چون تفکرکردم که این را بفهمم، در نظر من دشوار آمد. | ۱۶ 16 |
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
تابه قدسهای خدا داخل شدم. آنگاه در آخرت ایشان تامل کردم. | ۱۷ 17 |
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
هر آینه ایشان را در جایهای لغزنده گذاردهای. ایشان را به خرابیها خواهی انداخت. | ۱۸ 18 |
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
چگونه بغته به هلاکت رسیدهاند! تباه شده، از ترسهای هولناک نیست گردیدهاند. | ۱۹ 19 |
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
مثل خواب کسی چون بیدار شد، ای خداوندهمچنین چون برخیزی، صورت ایشان را ناچیزخواهی شمرد. | ۲۰ 20 |
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
لیکن دل من تلخ شده بود و در اندرون خود، دل ریش شده بودم. | ۲۱ 21 |
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
و من وحشی بودم ومعرفت نداشتم و مثل بهایم نزد تو گردیدم. | ۲۲ 22 |
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
ولی من دائم با تو هستم. تو دست راست مراتایید کردهای. | ۲۳ 23 |
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
موافق رای خود مرا هدایت خواهی نمود و بعد از این مرا به جلال خواهی رسانید. | ۲۴ 24 |
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
کیست برای من در آسمان؟ و غیر ازتو هیچچیز را در زمین نمی خواهم. | ۲۵ 25 |
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
اگرچه جسد و دل من زائل گردد، لیکن صخره دلم وحصه من خداست تا ابدالاباد. | ۲۶ 26 |
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
زیرا آنانی که ازتو دورند هلاک خواهند شد. و آنانی را که از توزنا میکنند، نابود خواهی ساخت. | ۲۷ 27 |
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
و اما مرانیکوست که به خدا تقرب جویم. بر خداوندیهوه توکل کردهام تا همه کارهای تو را بیان کنم. | ۲۸ 28 |
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.