< مزامیر 73 >

مزمور آساف هرآینه خدا برای اسرائیل نیکوست، یعنی برای آنانی که پاک دل هستند. ۱ 1
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
واما من نزدیک بود که پایهایم از راه در رود ونزدیک بود که قدمهایم بلغزد. ۲ 2
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
زیرا بر متکبران حسد بردم چون سلامتی شریران را دیدم. ۳ 3
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
زیراکه در موت ایشان قیدها نیست و قوت ایشان مستحکم است. ۴ 4
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
مثل مردم در زحمت نیستند ومثل آدمیان مبتلا نمی باشند. ۵ 5
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
بنابراین گردن ایشان به تکبر آراسته است وظلم مثل لباس ایشان را می‌پوشاند. ۶ 6
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
چشمان ایشان از فربهی بدر‌آمده است و از خیالات دل خود تجاوز می‌کنند. ۷ 7
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
استهزا می‌کنند و حرفهای بد می‌زنند و سخنان ظلم آمیز را از جای بلندمی گویند. ۸ 8
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
دهان خود را بر آسمانها گذارده‌اند وزبان ایشان در جهان گردش می‌کند. ۹ 9
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
پس قوم او بدینجا برمی گردند و آبهای فراوان، بدیشان نوشانیده می‌شود. ۱۰ 10
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
و ایشان می‌گویند: «خدا چگونه بداند و آیا حضرت اعلی علم دارد؟» ۱۱ 11
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
اینک اینان شریر هستند که همیشه مطمئن بوده، در دولتمندی افزوده می‌شوند. ۱۲ 12
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
یقین من دل خود را عبث طاهر ساخته و دستهای خود رابه پاکی شسته‌ام. ۱۳ 13
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
و من تمامی روز مبتلامی شوم و تادیب من هر بامداد حاضر است. ۱۴ 14
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
اگر می‌گفتم که چنین سخن گویم، هر آینه برطبقه فرزندان تو خیانت می‌کردم. ۱۵ 15
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
چون تفکرکردم که این را بفهمم، در نظر من دشوار آمد. ۱۶ 16
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
تابه قدسهای خدا داخل شدم. آنگاه در آخرت ایشان تامل کردم. ۱۷ 17
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
هر آینه ایشان را در جایهای لغزنده گذارده‌ای. ایشان را به خرابیها خواهی انداخت. ۱۸ 18
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
چگونه بغته به هلاکت رسیده‌اند! تباه شده، از ترسهای هولناک نیست گردیده‌اند. ۱۹ 19
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
مثل خواب کسی چون بیدار شد، ای خداوندهمچنین چون برخیزی، صورت ایشان را ناچیزخواهی شمرد. ۲۰ 20
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
لیکن دل من تلخ شده بود و در اندرون خود، دل ریش شده بودم. ۲۱ 21
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
و من وحشی بودم ومعرفت نداشتم و مثل بهایم نزد تو گردیدم. ۲۲ 22
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
ولی من دائم با تو هستم. تو دست راست مراتایید کرده‌ای. ۲۳ 23
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
موافق رای خود مرا هدایت خواهی نمود و بعد از این مرا به جلال خواهی رسانید. ۲۴ 24
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
کیست برای من در آسمان؟ و غیر ازتو هیچ‌چیز را در زمین نمی خواهم. ۲۵ 25
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
اگرچه جسد و دل من زائل گردد، لیکن صخره دلم وحصه من خداست تا ابدالاباد. ۲۶ 26
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
زیرا آنانی که ازتو دورند هلاک خواهند شد. و آنانی را که از توزنا می‌کنند، نابود خواهی ساخت. ۲۷ 27
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
و اما مرانیکوست که به خدا تقرب جویم. بر خداوندیهوه توکل کرده‌ام تا همه کارهای تو را بیان کنم. ۲۸ 28
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< مزامیر 73 >