< مزامیر 68 >

برای سالار مغنیان. مزمور و سرود داود خدا برخیزد و دشمنانش پراکنده شوند! و آنانی که از او نفرت دارند ازحضورش بگریزند! ۱ 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
چنانکه دود پراکنده می‌شود، ایشان را پراکنده ساز، و چنانکه موم پیش آتش گداخته می‌شود، همچنان شریران به حضور خدا هلاک گردند. ۲ 2
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
اما صالحان شادی کنند و در حضور خدا به وجد آیند و به شادمانی خرسند شوند. ۳ 3
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
برای خدا سرود بخوانید و به نام او ترنم نمایید و راهی درست کنید برای او که در صحراها سوار است. نام او یهوه است! به حضورش به وجد آیید! ۴ 4
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
پدر یتیمان و داور بیوه‌زنان، خداست در مسکن قدس خود! ۵ 5
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
خدا بی‌کسان را ساکن خانه می‌گرداند واسیران را به رستگاری بیرون می‌آورد، لیکن فتنه انگیزان در زمین تفتیده ساکن خواهند شد. ۶ 6
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
‌ای خدا هنگامی که پیش روی قوم خود بیرون رفتی، هنگامی که در صحرا خرامیدی، سلاه. ۷ 7
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
زمین متزلزل شد و آسمان به حضور خدا بارید. این سینا نیز از حضور خدا، خدای اسرائیل. ۸ 8
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
‌ای خدا باران نعمت‌ها بارانیدی و میراثت را چون خسته بود مستحکم گردانیدی. ۹ 9
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
جماعت تو درآن ساکن شدند. ای خدا، به جود خویش برای مساکین تدارک دیده‌ای. ۱۰ 10
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
خداوند سخن را می‌دهد. مبشرات انبوه عظیمی می‌شوند. ۱۱ 11
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
ملوک لشکرها فرار کرده، منهزم می‌شوند. و زنی که در خانه مانده است، غارت را تقسیم می‌کند. ۱۲ 12
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
اگرچه در آغلهاخوابیده بودید، لیکن مثل بالهای فاخته شده ایدکه به نقره پوشیده است و پرهایش به طلای سرخ. ۱۳ 13
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
چون قادر مطلق پادشاهان را در آن پراکنده ساخت، مثل برف بر صلمون درخشان گردید. ۱۴ 14
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
کوه خدا، کوه باشان است، کوهی با قله های افراشته کوه باشان است. ۱۵ 15
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
‌ای کوههای باقله های افراشته، چرا نگرانید؟ بر این کوهی که خدا برای مسکن خود برگزیده است هر آینه خداوند در آن تا به ابد ساکن خواهد بود. ۱۶ 16
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
ارابه های خدا کرورها و هزارهاست. خداونددر میان آنهاست و سینا در قدس است. ۱۷ 17
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
براعلی علیین صعود کرده، و اسیران را به اسیری برده‌ای. از آدمیان بخششها گرفته‌ای. بلکه ازفتنه انگیزان نیز تا یهوه خدا در ایشان مسکن گیرد. ۱۸ 18
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
متبارک باد خداوندی که هر روزه متحمل بارهای ما می‌شود و خدایی که نجات ماست، سلاه. ۱۹ 19
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
خدا برای ما، خدای نجات است ومفرهای موت از آن خداوند یهوه است. ۲۰ 20
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
هرآینه خدا سردشمنان خود را خرد خواهد کوبیدو کله مویدار کسی را که در گناه خود سالک باشد. ۲۱ 21
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
خداوند گفت: «از باشان باز خواهم آورد. از ژرفیهای دریا باز خواهم آورد. ۲۲ 22
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
تا پای خودرا در خون فروبری و زبان سگان تو از دشمنانت بهره خود را بیابد.» ۲۳ 23
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
‌ای خدا طریق های تو رادیده‌اند یعنی طریق های خدا و پادشاه مرا درقدس. ۲۴ 24
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
در‌پیش رو، مغنیان می‌خرامند و درعقب، سازندگان. و در وسط دوشیزگان دف زن. ۲۵ 25
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
خدا را در جماعت‌ها متبارک خوانید وخداوند را از چشمه اسرائیل. ۲۶ 26
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
آنجاست بنیامین صغیر، حاکم ایشان و روسای یهودامحفل ایشان. روسای زبولون و روسای نفتالی. ۲۷ 27
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
خدایت برای تو قوت را امر فرموده است. ای خدا آنچه را که برای ما کرده‌ای، استوار گردان. ۲۸ 28
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
به‌سبب هیکل تو که در اورشلیم است، پادشاهان هدایا نزد تو خواهند‌آورد. ۲۹ 29
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
و وحش نی زار را توبیخ فرما و رمه گاوان را با گوساله های قوم که با شمشهای نقره نزد تو گردن می‌نهند. وقوم هایی که جنگ را دوست می‌دارند پراکنده ساخته است. ۳۰ 30
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
سروران از مصر خواهند آمد وحبشه دستهای خود را نزد خدا بزودی درازخواهد کرد. ۳۱ 31
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
‌ای ممالک جهان برای خدا سرود بخوانید. برای خداوند سرود بخوانید، سلاه. ۳۲ 32
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
برای او که بر فلک الافلاک قدیمی سوار است. اینک آواز خود را می‌دهد آوازی که پرقوت است. ۳۳ 33
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
خدارا به قوت توصیف نمایید. جلال وی بر اسرائیل است و قوت او در افلاک. ۳۴ 34
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
‌ای خدا از قدسهای خود مهیب هستی. خدای اسرائیل قوم خود راقوت و عظمت می‌دهد. متبارک باد خدا. ۳۵ 35
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< مزامیر 68 >