< مزامیر 55 >

برای سالار مغنیان. قصیده داود بر ذوات اوتار ای خدا به دعای من گوش بگیر! و خودرا از تضرع من پنهان مکن! ۱ 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
به من گوش فراگیر و مرا مستجاب فرما! زیرا که در تفکر خودمتحیرم و ناله می‌کنم. ۲ 2
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
از آواز دشمن و به‌سبب ظلم شریر، زیرا که ظلم بر من می‌اندازند وبا خشم بر من جفا می‌کنند. ۳ 3
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
دل من در اندرونم پیچ و تاب می کند، و ترسهای موت بر من افتاده است. ۴ 4
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
ترس و لرز به من در‌آمده است. وحشتی هولناک مرا در‌گرفته است. ۵ 5
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
و گفتم کاش که مرابالها مثل کبوتر می‌بود تا پرواز کرده، استراحت می‌یافتم. ۶ 6
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
هرآینه بجای دور می‌پریدم، و درصحرا ماوا می‌گزیدم، سلاه. ۷ 7
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
می‌شتافتم بسوی پناهگاهی، از باد تند و از طوفان شدید. ۸ 8
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
‌ای خداوند آنها را هلاک کن و زبانهایشان راتفریق نما زیرا که در شهر ظلم و جنگ دیده‌ام. ۹ 9
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
روز و شب بر حصارهایش گردش می‌کنند وشرارت و مشقت در میانش می‌باشد. ۱۰ 10
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
فسادهادر میان وی است و جور و حیله از کوچه هایش دور نمی شود. ۱۱ 11
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
زیرا دشمن نبود که مرا ملامت می‌کرد والا تحمل می‌کردم؛ و خصم من نبود که بر من سربلندی می‌نمود؛ والا خود را از وی پنهان می‌ساختم. ۱۲ 12
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
بلکه تو بودی‌ای مرد نظیر من! ای یار خالص و دوست صدیق من! ۱۳ 13
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
که با یکدیگرمشورت شیرین می‌کردیم و به خانه خدا در انبوه می‌خرامیدیم. ۱۴ 14
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
موت بر ایشان ناگهان آید وزنده بگور فرو روند. زیرا شرارت در مسکن های ایشان و در میان ایشان است. (Sheol h7585) ۱۵ 15
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
و اما من نزد خدا فریاد می‌کنم و خداوندمرا نجات خواهد داد. ۱۶ 16
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
شامگاهان و صبح وظهر شکایت و ناله می‌کنم و او آواز مرا خواهدشنید. ۱۷ 17
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
جانم را از جنگی که بر من شده بود، بسلامتی فدیه داده است. زیرا بسیاری با من مقاومت می‌کردند. ۱۸ 18
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
خدا خواهد شنید و ایشان را جواب خواهد داد، او که از ازل نشسته است، سلاه. زیراکه در ایشان تبدیلها نیست و از خدانمی ترسند. ۱۹ 19
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
دست خود را بر صلح اندیشان خویش دراز کرده، و عهد خویش را شکسته است. ۲۰ 20
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
سخنان چرب زبانش نرم، لیکن دلش جنگ است. سخنانش چرب تر از روغن لیکن شمشیرهای برهنه است. ۲۱ 21
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
نصیب خود را به خداوند بسپار و تو را رزق خواهد داد. او تا به ابدنخواهد گذاشت که مرد عادل جنبش خورد. ۲۲ 22
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
وتو‌ای خدا ایشان را به چاه هلاکت فرو خواهی آورد. مردمان خون ریز و حیله ساز، روزهای خودرا نیمه نخواهند کرد، لیکن من بر تو توکل خواهم داشت. ۲۳ 23
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< مزامیر 55 >