< مزامیر 132 >
سرود درجات ای خداوند برای داود به یاد آور، همه مذلتهای او را. | ۱ 1 |
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
چگونه برای خداوند قسم خورد و برای قادر مطلق یعقوب نذر نمود | ۲ 2 |
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
که به خیمه خانه خود هرگز داخل نخواهم شد، و بر بستر تختخواب خود برنخواهم آمد. | ۳ 3 |
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
خواب به چشمان خود نخواهم داد و نه پینکی به مژگان خویش، | ۴ 4 |
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
تا مکانی برای خداوندپیدا کنم و مسکنی برای قادر مطلق یعقوب. | ۵ 5 |
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
اینک ذکر آن را در افراته شنیدیم و آن را درصحرای یعاریم یافتیم. | ۶ 6 |
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
به مسکن های او داخل شویم و نزد قدمگاه وی پرستش نماییم. | ۷ 7 |
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
ای خداوند به آرامگاه خود برخیز و بیا، تو و تابوت قوت تو. | ۸ 8 |
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
کاهنان تو به عدالت ملبس شوند ومقدسانت ترنم نمایند. | ۹ 9 |
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
بهخاطر بنده خودداود، روی مسیح خود را برمگردان. | ۱۰ 10 |
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
خداوند برای داود به راستی قسم خورد و از آن برنخواهدگشت که «از ثمره صلب تو بر تخت تو خواهم گذاشت. | ۱۱ 11 |
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
اگر پسران تو عهد مرا نگاه دارند وشهادتم را که بدیشان میآموزم، پسران ایشان نیزبر کرسی تو تا به ابد خواهند نشست.» | ۱۲ 12 |
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
زیرا که خداوند صهیون را برگزیده است وآن را برای مسکن خویش مرغوب فرموده. | ۱۳ 13 |
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
«این است آرامگاه من تا ابدالاباد. اینجا ساکن خواهم بود زیرا در این رغبت دارم. | ۱۴ 14 |
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
آذوقه آن را هرآینه برکت خواهم داد و فقیرانش را به نان سیر خواهم ساخت، | ۱۵ 15 |
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
و کاهنانش را به نجات ملبس خواهم ساخت و مقدسانش هرآینه ترنم خواهند نمود. | ۱۶ 16 |
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
در آنجا شاخ داود را خواهم رویانید و چراغی برای مسیح خود آماده خواهم ساخت. | ۱۷ 17 |
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
دشمنان او را به خجالت ملبس خواهم ساخت و تاج او بر وی شکوفه خواهدآورد.» | ۱۸ 18 |
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”