< مزامیر 132 >

سرود درجات ای خداوند برای داود به یاد آور، همه مذلتهای او را. ۱ 1
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
چگونه برای خداوند قسم خورد و برای قادر مطلق یعقوب نذر نمود ۲ 2
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
که به خیمه خانه خود هرگز داخل نخواهم شد، و بر بستر تختخواب خود برنخواهم آمد. ۳ 3
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
خواب به چشمان خود نخواهم داد و نه پینکی به مژگان خویش، ۴ 4
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
تا مکانی برای خداوندپیدا کنم و مسکنی برای قادر مطلق یعقوب. ۵ 5
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
اینک ذکر آن را در افراته شنیدیم و آن را درصحرای یعاریم یافتیم. ۶ 6
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
به مسکن های او داخل شویم و نزد قدمگاه وی پرستش نماییم. ۷ 7
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
‌ای خداوند به آرامگاه خود برخیز و بیا، تو و تابوت قوت تو. ۸ 8
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
کاهنان تو به عدالت ملبس شوند ومقدسانت ترنم نمایند. ۹ 9
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
به‌خاطر بنده خودداود، روی مسیح خود را برمگردان. ۱۰ 10
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
خداوند برای داود به راستی قسم خورد و از آن برنخواهدگشت که «از ثمره صلب تو بر تخت تو خواهم گذاشت. ۱۱ 11
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
اگر پسران تو عهد مرا نگاه دارند وشهادتم را که بدیشان می‌آموزم، پسران ایشان نیزبر کرسی تو تا به ابد خواهند نشست.» ۱۲ 12
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
زیرا که خداوند صهیون را برگزیده است وآن را برای مسکن خویش مرغوب فرموده. ۱۳ 13
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
«این است آرامگاه من تا ابدالاباد. اینجا ساکن خواهم بود زیرا در این رغبت دارم. ۱۴ 14
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
آذوقه آن را هرآینه برکت خواهم داد و فقیرانش را به نان سیر خواهم ساخت، ۱۵ 15
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
و کاهنانش را به نجات ملبس خواهم ساخت و مقدسانش هرآینه ترنم خواهند نمود. ۱۶ 16
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
در آنجا شاخ داود را خواهم رویانید و چراغی برای مسیح خود آماده خواهم ساخت. ۱۷ 17
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
دشمنان او را به خجالت ملبس خواهم ساخت و تاج او بر وی شکوفه خواهدآورد.» ۱۸ 18
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”

< مزامیر 132 >