< مزامیر 109 >

برای سالار مغنیان. مزمور داودای خدای تسبیح من، خاموش مباش! ۱ 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
زیرا که دهان شرارت ودهان فریب را بر من گشوده‌اند، و به زبان دروغ برمن سخن گفته‌اند. ۲ 2
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
به سخنان کینه مرا احاطه کرده‌اند و بی‌سبب با من جنگ نموده‌اند. ۳ 3
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
به عوض محبت من، با من مخالفت می‌کنند، و اما من دعا. ۴ 4
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
و به عوض نیکویی به من بدی کرده‌اند. و به عوض محبت، عداوت نموده. ۵ 5
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
مردی شریر را براو بگمار، و دشمن به‌دست راست او بایستد. ۶ 6
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
هنگامی که در محاکمه بیاید، خطا کار بیرون آیدو دعای او گناه بشود. ۷ 7
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
ایام عمرش کم شود ومنصب او را دیگری ضبط نماید. ۸ 8
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
فرزندان اویتیم بشوند و زوجه وی بیوه گردد. ۹ 9
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
و فرزندان او آواره شده، گدایی بکنند و از خرابه های خودقوت را بجویند. ۱۰ 10
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
طلبکار تمامی مایملک او را ضبط نماید و اجنبیان محنت او را تاراج کنند. ۱۱ 11
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
کسی نباشد که بر او رحمت کند و بر یتیمان وی احدی رافت ننماید. ۱۲ 12
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
ذریت وی منقطع گردند و در طبقه بعد نام ایشان محو شود. ۱۳ 13
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
عصیان پدرانش نزد خداوند به یاد آورده شودو گناه مادرش محو نگردد. ۱۴ 14
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
و آنها در مد نظرخداوند دائم بماند تا یادگاری ایشان را از زمین ببرد. ۱۵ 15
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
زیرا که رحمت نمودن را به یاد نیاورد، بلکه بر فقیر و مسکین جفا کرد و بر شکسته دل تااو را به قتل رساند. ۱۶ 16
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
چون که لعنت را دوست می‌داشت بدو رسیده و چون که برکت رانمی خواست، از او دور شده است. ۱۷ 17
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
و لعنت رامثل ردای خود در بر‌گرفت و مثل آب به شکمش درآمد و مثل روغن در استخوانهای وی. ۱۸ 18
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
پس مثل جامه‌ای که او را می‌پوشاند، و چون کمربندی که به آن همیشه بسته می‌شود، خواهدبود. ۱۹ 19
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
این است اجرت مخالفانم از جانب خداوند و برای آنانی که بر جان من بدی می‌گویند. ۲۰ 20
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
اما تو‌ای یهوه خداوند به‌خاطر نام خود بامن عمل نما؛ چون که رحمت تو نیکوست، مراخلاصی ده. ۲۱ 21
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
زیرا که من فقیر و مسکین هستم ودل من در اندرونم مجروح است. ۲۲ 22
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
مثل سایه‌ای که در زوال باشد رفته‌ام و مثل ملخ رانده شده‌ام. ۲۳ 23
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
زانوهایم از روزه داشتن می‌لرزد و گوشتم ازفربهی کاهیده می‌شود. ۲۴ 24
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
و من نزد ایشان عارگردیده‌ام. چون مرا می‌بینند سر خود رامی جنبانند. ۲۵ 25
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
‌ای یهوه خدای من مرا اعانت فرما، و به حسب رحمت خود مرا نجات ده، ۲۶ 26
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
تا بدانند که این است دست تو، و تو‌ای خداوند این را کرده‌ای. ۲۷ 27
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
ایشان لعنت بکنند، اما تو برکت بده. ایشان برخیزند و خجل گردند و اما بنده توشادمان شود. ۲۸ 28
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
جفا کنندگانم به رسوایی ملبس شوند و خجالت خویش را مثل ردا بپوشند. ۲۹ 29
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
خداوند را به زبان خود بسیار تشکر خواهم کرد و او را در جماعت کثیر حمد خواهم گفت. ۳۰ 30
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
زیرا که به‌دست راست مسکین خواهد ایستادتا او را از آنانی که بر جان او فتوا می‌دهندبرهاند. ۳۱ 31
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< مزامیر 109 >