< امثال 1 >

امثال سلیمان بن داود پادشاه اسرائیل ۱ 1
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
به جهت دانستن حکمت و عدل، و برای فهمیدن کلمات فطانت. ۲ 2
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
به جهت اکتساب ادب معرفت آمیز، و عدالت و انصاف و استقامت. ۳ 3
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
تاساده دلان را زیرکی بخشد، و جوانان را معرفت وتمیز. ۴ 4
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
تا مرد حکیم بشنود و علم را بیفزاید. ومرد فهیم تدابیر را تحصیل نماید. ۵ 5
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
تا امثال وکنایات را بفهمند، کلمات حکیمان و غوامض ایشان را. ۶ 6
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
ترس یهوه آغاز علم است. لیکن جاهلان حکمت و ادب را خوار می‌شمارند. ۷ 7
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
‌ای پسر من تادیب پدر خود را بشنو، و تعلیم مادر خویش را ترک منما. ۸ 8
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
زیرا که آنها تاج زیبایی برای سر تو، و جواهر برای گردن توخواهد بود. ۹ 9
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
‌ای پسر من اگر گناهکاران تو رافریفته سازند، قبول منما. ۱۰ 10
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
اگر گویند: «همراه مابیا تا برای خون در کمین بنشینیم، و برای بی‌گناهان بی‌جهت پنهان شویم، ۱۱ 11
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
مثل هاویه ایشان را زنده خواهیم بلعید، و تندرست مانندآنانی که به گور فرو می‌روند. (Sheol h7585) ۱۲ 12
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
هر گونه اموال نفیسه را پیدا خواهیم نمود. و خانه های خود را ازغنیمت مملو خواهیم ساخت. ۱۳ 13
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
قرعه خود رادر میان ما بینداز. و جمیع ما را یک کیسه خواهدبود.» ۱۴ 14
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
‌ای پسر من با ایشان در راه مرو. و پای خودرا از طریقهای ایشان باز دار ۱۵ 15
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
زیرا که پایهای ایشان برای شرارت می‌دود و به جهت ریختن خون می‌شتابد. ۱۶ 16
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
به تحقیق، گستردن دام در نظرهر بالداری بی‌فایده است. ۱۷ 17
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
لیکن ایشان به جهت خون خود کمین می‌سازند، و برای جان خویش پنهان می‌شوند. ۱۸ 18
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
همچنین است راههای هر کس که طماع سود باشد، که آن جان مالک خود را هلاک می‌سازد. ۱۹ 19
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
حکمت در بیرون ندا می‌دهد و در شوارع عام آواز خود را بلند می‌کند. ۲۰ 20
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
در سرچهارراهها در دهنه دروازه‌ها می‌خواند و در شهربه سخنان خود متکلم می‌شود ۲۱ 21
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
که «ای جاهلان تا به کی جهالت را دوست خواهید داشت؟ و تا به کی مستهزئین از استهزا شادی می‌کنند و احمقان از معرفت نفرت می‌نمایند؟ ۲۲ 22
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
به‌سبب عتاب من بازگشت نمایید. اینک روح خود را بر شما افاضه خواهم نمود و کلمات خود را بر شما اعلام خواهم کرد. ۲۳ 23
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
زیرا که چون خواندم، شما ابانمودید و دستهای خود را افراشتم و کسی اعتنانکرد. ۲۴ 24
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
بلکه تمامی نصیحت مرا ترک نمودید وتوبیخ مرا نخواستید. ۲۵ 25
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
پس من نیز در حین مصیبت شما خواهم خندید و چون ترس بر شمامستولی شود استهزا خواهم نمود. ۲۶ 26
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
چون خوف مثل باد تند بر شما عارض شود، و مصیبت مثل گردباد به شما دررسد، حینی که تنگی وضیق بر شما آید. ۲۷ 27
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
آنگاه مرا خواهند خواندلیکن اجابت نخواهم کرد، و صبحگاهان مراجستجو خواهند نمود اما مرا نخواهند یافت. ۲۸ 28
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
چونکه معرفت را مکروه داشتند، و ترس خداوند را اختیار ننمودند، ۲۹ 29
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
و نصیحت مراپسند نکردند، و تمامی توبیخ مرا خوار شمردند، ۳۰ 30
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
بنابراین، از میوه طریق خود خواهند خورد، واز تدابیر خویش سیر خواهند شد. ۳۱ 31
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
زیرا که ارتداد جاهلان، ایشان را خواهد کشت و راحت غافلانه احمقان، ایشان را هلاک خواهد ساخت. ۳۲ 32
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
اما هر‌که مرا بشنود در امنیت ساکن خواهدبود، و از ترس بلا مستریح خواهد ماند.» ۳۳ 33
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< امثال 1 >