< متّی 14 >
در آن هنگام هیرودیس تیترارخ چون شهرت عیسی را شنید، | ۱ 1 |
A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu.
به خادمان خود گفت: «این است یحیی تعمیددهنده که ازمردگان برخاسته است، و از این جهت معجزات از او صادر میگردد.» | ۲ 2 |
Ya ce wa barorinsa, “Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa”.
زیرا که هیرودیس یحیی را بخاطر هیرودیا، زن برادر خود فیلپس گرفته، در بند نهاده و در زندان انداخته بود؛ | ۳ 3 |
Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus.
چون که یحیی بدو همی گفت: «نگاه داشتن وی بر تو حلال نیست.» | ۴ 4 |
Ya ce masa, “Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba.”
و وقتی که قصد قتل او کرد، از مردم ترسید زیرا که او را نبی میدانستند. | ۵ 5 |
Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.
اما چون بزم میلاد هیرودیس را میآراستند، دختر هیرودیا درمجلس رقص کرده، هیرودیس را شاد نمود. | ۶ 6 |
Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus.
از اینرو قسم خورده، وعده داد که آنچه خواهدبدو بدهد. | ۷ 7 |
Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.
و او از ترغیب مادر خود گفت که «سریحیی تعمیددهنده را الان در طبقی به من عنایت فرما.» | ۸ 8 |
Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, “Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire.
آنگاه پادشاه برنجید، لیکن بجهت پاس قسم و خاطر همنشینان خود، فرمود که بدهند. | ۹ 9 |
Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.
و فرستاده، سر یحیی را در زندان از تن جدا کرد، | ۱۰ 10 |
Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku.
و سر او را در طشتی گذارده، به دختر تسلیم نمودند و او آن را نزد مادر خود برد. | ۱۱ 11 |
Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta.
پس شاگردانش آمده، جسد او را برداشته، به خاک سپردند و رفته، عیسی را اطلاع دادند. | ۱۲ 12 |
Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.
و چون عیسی این را شنید، به کشتی سوارشده، از آنجا به ویرانهای به خلوت رفت. و چون مردم شنیدند، از شهرها به راه خشکی از عقب وی روانه شدند. | ۱۳ 13 |
Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen.
پس عیسی بیرون آمده، گروهی بسیار دیده، بر ایشان رحم فرمود وبیماران ایشان را شفا داد. | ۱۴ 14 |
Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.
و در وقت عصر، شاگردانش نزد وی آمده، گفتند: «این موضع ویرانه است و وقت الان گذشته. پس این گروه رامرخص فرما تا به دهات رفته بجهت خود غذابخرند.» | ۱۵ 15 |
Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, “Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci.”
عیسی ایشان را گفت: «احتیاج به رفتن ندارند. شما ایشان را غذا دهید.» | ۱۶ 16 |
Amma Yesu ya ce masu, “Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci.”
بدو گفتند: «در اینجا جز پنج نان و دو ماهی نداریم!» | ۱۷ 17 |
Suka ce masa, “Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai.”
گفت: «آنها را اینجا به نزد من بیاورید!» | ۱۸ 18 |
Yesu ya ce, “Ku kawo mani su.”
وبدان جماعت فرمود تا بر سبزه نشستند و پنج نان و دو ماهی را گرفته، به سوی آسمان نگریسته، برکت داد و نان را پاره کرده، به شاگردان سپرد وشاگردان بدان جماعت. | ۱۹ 19 |
Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron.
و همه خورده، سیر شدند و از پاره های باقیمانده دوازده سبد پرکرده، برداشتند. | ۲۰ 20 |
Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike.
و خورندگان سوای زنان واطفال قریب به پنج هزار مرد بودند. | ۲۱ 21 |
Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.
بیدرنگ عیسی شاگردان خود را اصرارنمود تا به کشتی سوار شده، پیش از وی به کناره دیگر روانه شوند تا آن گروه را رخصت دهد. | ۲۲ 22 |
Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron.
وچون مردم را روانه نمود، به خلوت برای عبادت بر فراز کوهی برآمد. و وقت شام در آنجا تنها بود. | ۲۳ 23 |
Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai.
اما کشتی در آن وقت در میان دریا بهسبب بادمخالف که میوزید، به امواج گرفتار بود. | ۲۴ 24 |
Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.
و درپاس چهارم از شب، عیسی بر دریا خرامیده، به سوی ایشان روانه گردید. | ۲۵ 25 |
Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku.
اما چون شاگردان، او را بر دریا خرامان دیدند، مضطرب شده، گفتندکه خیالی است؛ و از خوف فریاد برآوردند. | ۲۶ 26 |
Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, “Fatalwa ce,” suka yi kururuwa cikin tsoro.
اماعیسی ایشان را بیتامل خطاب کرده، گفت: «خاطر جمع دارید! منم ترسان مباشید!» | ۲۷ 27 |
Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, “Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro.”
پطرس در جواب او گفت: «خداوندا، اگر تویی مرا بفرما تا بر روی آب، نزد تو آیم.» | ۲۸ 28 |
Bitrus ya amsa masa cewa, “Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan.”
گفت: «بیا!» در ساعت پطرس از کشتی فرود شده، برروی آب روانه شد تا نزد عیسی آید. | ۲۹ 29 |
Yesu yace, “Zo” Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu.
لیکن چون باد را شدید دید، ترسان گشت و مشرف به غرق شده، فریاد برآورده، گفت: «خداوندا مرادریاب.» | ۳۰ 30 |
Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
عیسی بیدرنگ دست آورده، او رابگرفت و گفت: «ای کمایمان، چرا شک آوردی؟» | ۳۱ 31 |
Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, “Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?”
و چون به کشتی سوار شدند، بادساکن گردید. | ۳۲ 32 |
Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa.
پس اهل کشتی آمده، او راپرستش کرده، گفتند: «فی الحقیقه تو پسر خدا هستی!» | ۳۳ 33 |
Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, “Hakika kai Dan Allah ne.”
آنگاه عبور کرده، به زمین جنیسره آمدند، | ۳۴ 34 |
Da suka haye, sun iso kasar Janisarata.
و اهل آن موضع او را شناخته، به همگی آن نواحی فرستاده، همه بیماران را نزد او آوردند، | ۳۵ 35 |
Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya.
و از او اجازت خواستند که محض دامن ردایش را لمس کنند و هرکه لمس کرد، صحت کامل یافت. | ۳۶ 36 |
Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.