< متّی 12 >

در آن زمان، عیسی در روز سبت از میان کشتزارها می‌گذشت و شاگردانش چون گرسنه بودند، به چیدن و خوردن خوشه هاآغاز کردند. ۱ 1
A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
اما فریسیان چون این را دیدند، بدوگفتند: «اینک شاگردان تو عملی می‌کنند که کردن آن در سبت جایز نیست.» ۲ 2
Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
ایشان را گفت: «مگرنخوانده‌اید آنچه داود و رفیقانش کردند، وقتی که گرسنه بودند؟ ۳ 3
Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
چه طور به خانه خدا در‌آمده، نانهای تقدمه را خورد که خوردن آن بر او ورفیقانش حلال نبود بلکه بر کاهنان فقط. ۴ 4
Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
یا درتورات نخوانده‌اید که در روزهای سبت، کهنه درهیکل سبت را حرمت نمی دارند و بی‌گناه هستند؟ ۵ 5
Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
لیکن به شما می‌گویم که در اینجاشخصی بزرگتر از هیکل است! ۶ 6
Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
و اگر این معنی را درک می‌کردید که رحمت می‌خواهم نه قربانی، بی‌گناهان را مذمت نمی نمودید. ۷ 7
In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
زیرا که پسرانسان مالک روز سبت نیز ا ست.» ۸ 8
Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
و از آنجا رفته، به کنیسه ایشان درآمد، ۹ 9
Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
که ناگاه شخص دست خشکی حاضر بود. پس ازوی پرسیده، گفتند: «آیا در روز سبت شفا دادن جایز است یا نه؟» تا ادعایی بر او وارد آورند. ۱۰ 10
Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
وی به ایشان گفت: «کیست از شما که یک گوسفند داشته باشد و هرگاه آن در روز سبت به حفره‌ای افتد، او را نخواهد گرفت و بیرون آورد؟ ۱۱ 11
Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
پس چقدر انسان از گوسفند افضل است. بنابراین در سبت‌ها نیکویی‌کردن روا است.» ۱۲ 12
Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
آنگاه آن مرد را گفت: «دست خود را دراز کن!» پس دراز کرده، مانند دیگری صحیح گردید. ۱۳ 13
Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
اما فریسیان بیرون رفته، بر او شورا نمودند که چطور او را هلاک کنند. ۱۴ 14
Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
عیسی این را درک نموده، از آنجا روانه شدو گروهی بسیار از عقب او آمدند. پس جمیع ایشان را شفا بخشید، ۱۵ 15
Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
و ایشان را قدغن فرمودکه او را شهرت ندهند. ۱۶ 16
Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
تا تمام گردد کلامی که به زبان اشعیای نبی گفته شده بود: ۱۷ 17
domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
«اینک بنده من که او را برگزیدم و حبیب من که خاطرم از وی خرسند است. روح خود را بر وی خواهم نهاد تاانصاف را بر امت‌ها اشتهار نماید. ۱۸ 18
“Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
نزاع و فغان نخواهد کرد و کسی آواز او را در کوچه هانخواهد شنید. ۱۹ 19
Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
نی خرد شده را نخواهد شکست و فتیله نیم‌سوخته را خاموش نخواهدکرد تا آنکه انصاف را به نصرت برآورد. ۲۰ 20
Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
و به نام او امت‌ها امید خواهند داشت.» ۲۱ 21
Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
آنگاه دیوانه‌ای کور و گنگ را نزد او آوردندو او را شفا داد چنانکه آن کور و گنگ، گویا و بیناشد. ۲۲ 22
Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
و تمام آن گروه در حیرت افتاده، گفتند: «آیا این شخص پسر داود نیست؟» ۲۳ 23
Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
لیکن فریسیان شنیده، گفتند: «این شخص دیوها رابیرون نمی کند مگر به یاری بعلزبول، رئیس دیوها!» ۲۴ 24
Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
عیسی خیالات ایشان را درک نموده، بدیشان گفت: «هر مملکتی که بر خود منقسم گردد، ویران شود و هر شهری یا خانه‌ای که برخود منقسم گردد، برقرار نماند. ۲۵ 25
Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
لهذا اگرشیطان، شیطان را بیرون کند، هرآینه بخلاف خودمنقسم گردد. پس چگونه سلطنتش پایدار ماند؟ ۲۶ 26
Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
و اگر من به وساطت بعلزبول دیوها را بیرون می‌کنم، پسران شما آنها را به یاری که بیرون می‌کنند؟ از این جهت ایشان بر شما داوری خواهند کرد. ۲۷ 27
Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
لیکن هرگاه من به روح خدادیوها را اخراج می‌کنم، هرآینه ملکوت خدا برشما رسیده است. ۲۸ 28
Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
و چگونه کسی بتواند درخانه شخصی زورآور درآید و اسباب او را غارت کند، مگر آنکه اول آن زورآور را ببندد و پس خانه او را تاراج کند؟ ۲۹ 29
Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
هر‌که با من نیست، برخلاف من است و هر‌که با من جمع نکند، پراکنده سازد. ۳۰ 30
Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
از این‌رو، شما را می‌گویم هر نوع گناه و کفر از انسان آمرزیده می‌شود، لیکن کفر به روح‌القدس از انسان عفو نخواهد شد. ۳۱ 31
Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
وهرکه برخلاف پسر انسان سخنی گوید، آمرزیده شود اما کسی‌که برخلاف روح‌القدس گوید، دراین عالم و در عالم آینده، هرگز آمرزیده نخواهدشد. (aiōn g165) ۳۲ 32
Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn g165)
یا درخت را نیکو گردانید و میوه‌اش رانیکو، یا درخت را فاسد سازید و میوه‌اش رافاسد، زیرا که درخت از میوه‌اش شناخته می‌شود. ۳۳ 33
Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
‌ای افعی‌زادگان، چگونه می‌توانیدسخن نیکو گفت و حال آنکه بد هستید زیرا که زبان از زیادتی دل سخن می‌گوید. ۳۴ 34
Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
مرد نیکو ازخزانه نیکوی دل خود، چیزهای خوب برمی آورد و مرد بد از خزانه بد، چیزهای بدبیرون می‌آورد. ۳۵ 35
Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
لیکن به شما می‌گویم که هرسخن باطل که مردم گویند، حساب آن را در روزداوری خواهند داد. ۳۶ 36
Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
زیرا که از سخنان خودعادل شمرده خواهی شد و از سخنهای تو بر توحکم خواهد شد.» ۳۷ 37
Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
آنگاه بعضی از کاتبان و فریسیان در جواب گفتند: «ای استاد می‌خواهیم از تو آیتی ببینیم.» ۳۸ 38
Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
او در جواب ایشان گفت: «فرقه شریر و زناکارآیتی می‌طلبند و بدیشان جز آیت یونس نبی داده نخواهد شد. ۳۹ 39
Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
زیرا همچنانکه یونس سه شبانه‌روز در شکم ماهی ماند، پسر انسان نیز سه شبانه‌روز در شکم زمین خواهد بود. ۴۰ 40
Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
مردمان نینوا درروز داوری با این طایفه برخاسته، بر ایشان حکم خواهند کرد زیرا که به موعظه یونس توبه کردند واینک بزرگتری از یونس در اینجا است. ۴۱ 41
Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
ملکه جنوب در روز داوری با این فرقه برخاسته، برایشان حکم خواهد کرد زیرا که از اقصای زمین آمد تا حکمت سلیمان را بشنود، و اینک شخصی بزرگتر از سلیمان در اینجا است. ۴۲ 42
Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
و وقتی که روح پلید از آدمی بیرون آید، درطلب راحت به‌جایهای بی‌آب گردش می‌کند ونمی یابد. ۴۳ 43
Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
پس می‌گوید “به خانه خود که از آن بیرون آمدم برمی گردم، “و چون آید، آن را خالی و جاروب شده و آراسته می‌بیند. ۴۴ 44
Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
آنگاه می‌رود و هفت روح دیگر بدتر از خود رابرداشته، می‌آورد و داخل گشته، ساکن آنجامی شوند و انجام آن شخص بدتر از آغازش می‌شود. همچنین به این فرقه شریر خواهد شد.» ۴۵ 45
Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
او با آن جماعت هنوز سخن می‌گفت که ناگاه مادر و برادرانش در طلب گفتگوی وی بیرون ایستاده بودند. ۴۶ 46
Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
و شخصی وی را گفت: «اینک مادر تو و برادرانت بیرون ایستاده، می‌خواهند باتو سخن گویند.» ۴۷ 47
Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
در جواب قایل گفت: «کیست مادر من و برادرانم کیانند؟» ۴۸ 48
Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
و دست خود را به سوی شاگردان خود دراز کرده، گفت: «اینانند مادر من و برادرانم. ۴۹ 49
Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
زیرا هر‌که اراده پدر مرا که در آسمان است به‌جا آورد، همان برادر و خواهر و مادر من است.» ۵۰ 50
Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”

< متّی 12 >