< لاویان 21 >

و خداوند به موسی گفت: «به کاهنان یعنی پسران هارون خطاب کرده، به ایشان بگو: کسی از شما برای مردگان، خود رانجس نسازد، ۱ 1
Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
جز برای خویشان نزدیک خود، یعنی برای مادرش و پدرش و پسرش و دخترش و برادرش. ۲ 2
sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
و برای خواهر باکره خود که قریب او باشد و شوهر ندارد؛ برای او خود را نجس تواند کرد. ۳ 3
ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
چونکه در قوم خود رئیس است، خود را نجس نسازد، تا خویشتن را بی‌عصمت نماید. ۴ 4
Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
سر خود را بی‌مو نسازند، و گوشه های ریش خود را نتراشند، و بدن خود را مجروح ننمایند. ۵ 5
“‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
برای خدای خود مقدس باشند، و نام خدای خود را بی‌حرمت ننمایند. زیرا که هدایای آتشین خداوند و طعام خدای خود را ایشان می‌گذرانند. پس مقدس باشند. ۶ 6
Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
زن زانیه یابی عصمت را نکاح ننمایند، و زن مطلقه ازشوهرش را نگیرند، زیرا او برای خدای خودمقدس است. ۷ 7
“‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
پس او را تقدیس نما، زیرا که اوطعام خدای خود را می‌گذراند. پس برای تومقدس باشد، زیرا من یهوه که شما را تقدیس می‌کنم، قدوس هستم. ۸ 8
An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
و دختر هر کاهنی که خود را به فاحشگی بی‌عصمت ساخته باشد، پدرخود را بی‌عصمت کرده است. به آتش سوخته شود. ۹ 9
“‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
«و آن که از میان برادرانش رئیس کهنه باشد، که بر سر او روغن مسح ریخته شده، وتخصیص گردیده باشد تا لباس را بپوشد، موی سر خود را نگشاید و گریبان خود را چاک نکند، ۱۰ 10
“‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
و نزد هیچ شخص مرده نرود، و برای پدر خودو مادر خود خویشتن را نجس نسازد. ۱۱ 11
Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
و ازمکان مقدس بیرون نرود، و مکان مقدس خدای خود را بی‌عصمت نسازد، زیرا که تاج روغن مسح خدای او بر وی می‌باشد. من یهوه هستم. ۱۲ 12
An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
و اوزن باکره‌ای نکاح کند. ۱۳ 13
“‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
و بیوه و مطلقه وبی عصمت و زانیه، اینها را نگیرد. فقط باکره‌ای از قوم خود را به زنی بگیرد. ۱۴ 14
Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
و ذریت خود را درمیان قوم خود بی‌عصمت نسازد. من یهوه هستم که او را مقدس می‌سازم.» ۱۵ 15
don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
و خداوند موسی را خطاب کرده، گفت: ۱۶ 16
Ubangiji ya ce wa Musa,
«هارون را خطاب کرده، بگو: هر کس از اولادتو در طبقات ایشان که عیب داشته باشد نزدیک نیاید، تا طعام خدای خود را بگذراند. ۱۷ 17
“Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
پس هرکس که عیب دارد نزدیک نیاید، نه مرد کور و نه لنگ و نه پهن بینی و نه زایدالاعضا، ۱۸ 18
Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
و نه کسی‌که شکسته پا یا شکسته دست باشد، ۱۹ 19
ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
و نه گوژپشت و نه کوتاه قد و نه کسی‌که در چشم خودلکه دارد، و نه صاحب جرب و نه کسی‌که گری دارد و نه شکسته بیضه. ۲۰ 20
ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
هر کس از اولاد هارون کاهن که عیب داشته باشد نزدیک نیاید، تا هدایای آتشین خداوند را بگذراند، چونکه معیوب است، برای گذرانیدن طعام خدای خود نزدیک نیاید. ۲۱ 21
Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
طعام خدای خود را خواه از آنچه قدس اقداس است و خواه از آنچه مقدس است، بخورد. ۲۲ 22
Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
لیکن به حجاب داخل نشود و به مذبح نزدیک نیاید، چونکه معیوب است، تا مکان مقدس مرا بی‌حرمت نسازد. من یهوه هستم که ایشان را تقدیس می‌کنم.» ۲۳ 23
duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
پس موسی هارون وپسرانش و تمامی بنی‌اسرائیل را چنین گفت. ۲۴ 24
Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.

< لاویان 21 >