< سوگنامه 4 >

چگونه طلا زنگ گرفته و زر خالص منقلب گردیده است؟ سنگهای قدس به‌سر هرکوچه ریخته شده است. ۱ 1
Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
چگونه پسران گرانبهای صهیون که به زر ناب برابر می‌بودند مثل ظروف سفالین که عمل دست کوزه‌گر باشد شمرده شده‌اند. ۲ 2
Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
شغالها تیز پستانهای خود را بیرون آورده، بچه های خویش را شیر می‌دهند. اما دختر قوم من مانند شتر مرغ بری، بیرحم گردیده است. ۳ 3
Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
زبان اطفال شیرخواره از تشنگی به کام ایشان می‌چسبد، و کودکان نان می‌خواهند وکسی به ایشان نمی دهد. ۴ 4
Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
آنانی که خوراک لذیذ می‌خورند در کوچه ها بینوا گشته‌اند. آنانی که در لباس قرمز تربیت یافته‌اند مزبله‌ها را در آغوش می‌کشند. ۵ 5
Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
زیرا که عصیان دختر قوم من از گناه سدوم زیاده است، که در لحظه‌ای واژگون شد و کسی دست بر او ننهاد. ۶ 6
Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
نذیرگان او از برف، صاف تر و از شیر، سفیدتر بودند. بدن ایشان از لعل سرختر و جلوه ایشان مثل یاقوت کبود بود. ۷ 7
’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
اما صورت ایشان از سیاهی سیاهتر شده است که در کوچه‌ها شناخته نمی شوند. پوست ایشان به استخوانهایشان چسبیده و خشک شده، مثل چوب گردیده است. ۸ 8
Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
کشتگان شمشیر از کشتگان گرسنگی بهترند. زیرا که اینان از عدم محصول زمین مجروح شده، کاهیده می‌گردند. ۹ 9
Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
زنان مهربان، اولاد خود را می‌پزند به‌دستهای خویش. و آنها در هلاکت دختر قوم من غذای ایشان هستند. ۱۰ 10
Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
خداوند غضب خود را به اتمام رسانیده، حدت خشم خویش را ریخته است، و آتشی درصهیون افروخته که اساس آن را سوزانیده است. ۱۱ 11
Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
پادشاهان جهان و جمیع سکنه ربع مسکون باور نمی کردند که عدو و دشمن به دروازه های اورشلیم داخل شود. ۱۲ 12
Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
به‌سبب گناه انبیا و گناه کاهنانش، که خون عادلان را در اندرونش ریختند. ۱۳ 13
Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
مثل کوران در کوچه‌ها نوان می‌شوند و ازخون نجس شده‌اند، که لباس ایشان را لمس نمی توانند کرد. ۱۴ 14
Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
و به ایشان ندا می‌کنند که دور شوید، نجس (هستید)! دور شوید دور شوید و لمس منمایید! چون فرار می‌کردند نوان می‌شدند و در میان امت‌ها می‌گفتند که در اینجا دیگر توقف نخواهند کرد. ۱۵ 15
“Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
خشم خداوند ایشان را پراکنده ساخته وایشان را دیگر منظور نخواهد داشت. به کاهنان ایشان اعتنا نمی کنند و بر مشایخ، رافت ندارند. ۱۶ 16
Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
چشمان ما تا حال در انتظار اعانت باطل ماکاهیده می‌شود. بر دیده بانگاههای خود انتظارکشیدیم، برای امتی که نجات نمی توانند داد. ۱۷ 17
Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
قدمهای ما را تعاقب نمودند به حدی که درکوچه های خود راه نمی توانیم رفت. آخرت مانزدیک است و روزهای ما تمام شده زیرا که اجل ما رسیده است. ۱۸ 18
Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
تعاقب کنندگان ما از عقابهای هواتیزروتراند. ما را بر کوهها تعاقب می‌کنند و برای ما در صحرا کمین می‌گذارند. ۱۹ 19
Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
مسیح خداوند که نفخه بینی ما می‌بود درحفره های ایشان گرفتار شد، که درباره اومی گفتم زیر سایه او در میان امت‌ها، زیست خواهیم نمود. ۲۰ 20
Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
مسرور باش و شادی کن‌ای دختر ادوم که در زمین عوص ساکن هستی! بر تو نیز این‌جام خواهد رسید و مست شده، عریان خواهی شد. ۲۱ 21
Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
‌ای دختر صهیون سزای گناه تو تمام شد وتو را دیگر جلای وطن نخواهد ساخت. ای دخترادوم، عقوبت گناه تو را به تو خواهد رسانید وگناهان تو را کشف خواهد نمود. ۲۲ 22
Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.

< سوگنامه 4 >