< یوشع 9 >

و واقع شد که تمامی ملوک حتیان و اموریان و کنعانیان و فرزیان و حویان و یبوسیان، که به آن طرف اردن در کوه و هامون و درتمامی کناره دریای بزرگ تا مقابل لبنان بودند، چون این را شنیدند، ۱ 1
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
با هم جمع شدند، تا بایوشع و اسرائیل متفق جنگ کنند. ۲ 2
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
و اما ساکنان جبعون چون آنچه را که یوشع به اریحا و عای کرده بود شنیدند، ۳ 3
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
ایشان نیز به حیله رفتار نمودند و روانه شده، خویشتن را مثل ایلچیان ظاهر کرده، جوالهای کهنه بر الاغهای خود و مشکهای شراب که کهنه و پاره و بسته شده بود، گرفتند. ۴ 4
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
و بر پایهای خود کفشهای مندرس و پینه زده و بر بدن خود رخت کهنه وتمامی نان توشه ایشان خشک و کفه زده بود. ۵ 5
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
ونزد یوشع به اردو در جلجال آمده، به او و به مردان اسرائیل گفتند که «از زمین دور آمده‌ایم پس الان با ما عهد ببندید.» ۶ 6
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
و مردان اسرائیل به حویان گفتند: «شاید در میان ما ساکن باشید. پس چگونه با شما عهد ببندیم؟» ۷ 7
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
ایشان به یوشع گفتند: «ما بندگان تو هستیم.» یوشع به ایشان گفت که «شما کیانید و از کجامی آیید؟» ۸ 8
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
به وی گفتند: «بندگانت به‌سبب اسم یهوه خدای تو از زمین بسیار دور آمده‌ایم زیرا که آوازه او و هر‌چه را که در مصر کرد، شنیدیم. ۹ 9
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
ونیز آنچه را به دو ملک اموریان که به آن طرف اردن بودند یعنی به سیهون، ملک حشبون، و عوج، ملک باشان، که در عشتاروت بود، کرد. ۱۰ 10
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
پس مشایخ ما و تمامی ساکنان زمین ما به ما گفتند که توشه‌ای به جهت راه به‌دست خود بگیرید و به استقبال ایشان رفته، ایشان را بگویید که ما بندگان شما هستیم. پس الان با ما عهد ببندید. ۱۱ 11
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
این نان ما در روزی که روانه شدیم تا نزد شما بیاییم از خانه های خود آن را برای توشه راه گرم گرفتیم، والان اینک خشک و کفه زده شده است. ۱۲ 12
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
و این مشکهای شراب که پر کردیم تازه بود واینک پاره شده، و این رخت و کفشهای ما از کثرت طول راه کهنه شده است.» ۱۳ 13
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
آنگاه آن مردمان از توشه ایشان گرفتند و از دهان خداوند مشورت نکردند. ۱۴ 14
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
و یوشع با ایشان صلح کرده، عهد بست که ایشان را زنده نگهدارد و روسای جماعت باایشان قسم خوردند. ۱۵ 15
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
اما بعد از انقضای سه روز که با ایشان عهدبسته بودند، شنیدند که آنها نزدیک ایشانند و درمیان ایشان ساکنند. ۱۶ 16
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
پس بنی‌اسرائیل کوچ کرده، در روز سوم به شهرهای ایشان رسیدند وشهرهای ایشان، جبعون و کفیره و بئیروت و قریه یعاریم، بود. ۱۷ 17
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
و بنی‌اسرائیل ایشان را نکشتندزیرا روسای جماعت برای ایشان به یهوه، خدای اسرائیل، قسم خورده بودند، و تمامی جماعت برروسا همهمه کردند. ۱۸ 18
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
و جمیع روسا به تمامی جماعت گفتند که برای ایشان به یهوه، خدای اسرائیل، قسم خوردیم پس الان نمی توانیم به ایشان ضرر برسانیم. ۱۹ 19
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
این را به ایشان خواهیم کرد و ایشان را زنده نگاه خواهیم داشت مبادا به‌سبب قسمی که برای ایشان خوردیم، غضب بر مابشود. ۲۰ 20
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
و روسا به ایشان گفتند: «بگذارید که زنده بمانند.» پس برای تمامی جماعت هیزم شکنان و سقایان آب شدند، چنانکه روسا به ایشان گفته بودند. ۲۱ 21
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
و یوشع ایشان را خواند و بدیشان خطاب کرده، گفت: «چرا ما را فریب دادید و گفتید که مااز شما بسیار دور هستیم و حال آنکه در میان ما ساکنید. ۲۲ 22
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
پس حال شما ملعونید و از شماغلامان و هیزم شکنان و سقایان آب همیشه برای خانه خدای ما خواهند بود.» ۲۳ 23
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
ایشان در جواب یوشع گفتند: «زیرا که بندگان تو را یقین خبر دادندکه یهوه، خدای تو، بنده خود موسی را امر کرده بود که تمامی این زمین را به شما بدهد، و همه ساکنان زمین را از پیش روی شما هلاک کنند، وبرای جانهای خود به‌سبب شما بسیار ترسیدیم، پس این کار را کردیم. ۲۴ 24
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
و الان، اینک ما در دست تو هستیم؛ به هر طوری که در نظر تو نیکو وصواب است که به ما رفتار نمایی، عمل نما.» ۲۵ 25
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
پس او با ایشان به همین طور عمل نموده، ایشان را از دست بنی‌اسرائیل رهایی داد که ایشان را نکشتند. ۲۶ 26
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
و یوشع در آن روز ایشان را مقررکرد تا هیزم شکنان و سقایان آب برای جماعت وبرای مذبح خداوند باشند، در مقامی که او اختیارکند و تا به امروز چنین هستند. ۲۷ 27
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< یوشع 9 >