< ایّوب 9 >

پس ایوب در جواب گفت: ۱ 1
Sai Ayuba ya amsa,
«یقین می‌دانم که چنین است. لیکن انسان نزد خدا چگونه عادل شمرده شود؟ ۲ 2
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
اگر بخواهد با وی منازعه نماید، یکی از هزار او را جواب نخواهد داد. ۳ 3
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
اودر ذهن حکیم و در قوت تواناست. کیست که با اومقاومت کرده و کامیاب شده باشد؟ ۴ 4
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
آنکه کوههارا منتقل می‌سازد و نمی فهمند، و در غضب خویش آنها را واژگون می‌گرداند، ۵ 5
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
که زمین را ازمکانش می‌جنباند، و ستونهایش متزلزل می‌شود. ۶ 6
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
که آفتاب را امر می‌فرماید و طلوع نمی کند وستارگان را مختوم می‌سازد. ۷ 7
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
که به تنهایی، آسمانها را پهن می‌کند و بر موجهای دریامی خرامد. ۸ 8
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
که دب اکبر و جبار و ثریا را آفرید، و برجهای جنوب را ۹ 9
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
که کارهای عظیم بی‌قیاس را می‌کند و کارهای عجیب بی‌شمار را. ۱۰ 10
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
اینک از من می‌گذرد و او را نمی بینم، و عبور می‌کند واو را احساس نمی نمایم. ۱۱ 11
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
اینک او می‌رباید وکیست که او را منع نماید؟ و کیست که به او تواندگفت: چه می‌کنی؟ ۱۲ 12
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
خدا خشم خود را بازنمی دارد و مددکاران رحب زیر او خم می‌شوند. ۱۳ 13
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
«پس به طریق اولی، من کیستم که او راجواب دهم و سخنان خود را بگزینم تا با اومباحثه نمایم؟ ۱۴ 14
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
که اگر عادل می‌بودم، او راجواب نمی دادم، بلکه نزد داور خود استغاثه می‌نمودم. ۱۵ 15
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
اگر او را می‌خواندم و مرا جواب می‌داد، باور نمی کردم که آواز مرا شنیده است. ۱۶ 16
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
زیرا که مرا به تندبادی خرد می‌کند و بی‌سبب، زخمهای مرا بسیار می‌سازد. ۱۷ 17
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
مرا نمی گذارد که نفس بکشم، بلکه مرا به تلخیها پر می‌کند. ۱۸ 18
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
اگردرباره قوت سخن گوییم، اینک او قادر است؛ واگر درباره انصاف، کیست که وقت را برای من تعیین کند؟ ۱۹ 19
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
اگر عادل می‌بودم دهانم مرا مجرم می‌ساخت، و اگر کامل می‌بودم مرا فاسق می‌شمرد. ۲۰ 20
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
اگر کامل هستم، خویشتن رانمی شناسم، و جان خود را مکروه می‌دارم. ۲۱ 21
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
این امر برای همه یکی است. بنابراین می‌گویم که اوصالح است و شریر را هلاک می‌سازد. ۲۲ 22
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
اگرتازیانه ناگهان بکشد، به امتحان بی‌گناهان استهزامی کند. ۲۳ 23
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
جهان به‌دست شریران داده شده است و روی حاکمانش را می‌پوشاند. پس اگر چنین نیست، کیست که می‌کند؟ ۲۴ 24
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
و روزهایم از پیک تیزرفتار تندروتر است، می‌گریزد و نیکویی رانمی بیند. ۲۵ 25
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
مثل کشتیهای تیزرفتار می‌گریزد و مثل عقاب که بر شکار فرود آید. ۲۶ 26
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
اگر فکر کنم که ناله خود را فراموش کنم و ترش رویی خود رادور کرده، گشاده رو شوم، ۲۷ 27
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
از تمامی مشقتهای خود می‌ترسم و می‌دانم که مرا بی‌گناه نخواهی شمرد، ۲۸ 28
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
چونکه ملزم خواهم شد. پس چرا بیجازحمت بکشم؟ ۲۹ 29
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
اگر خویشتن را به آب برف غسل دهم، و دستهای خود را به اشنان پاک کنم، ۳۰ 30
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
آنگاه مرا در لجن فرو می‌بری، و رختهایم مرامکروه می‌دارد. ۳۱ 31
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
زیرا که او مثل من انسان نیست که او را جواب بدهم و با هم به محاکمه بیاییم. ۳۲ 32
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
در میان ما حکمی نیست که بر هر دوی مادست بگذارد. ۳۳ 33
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
کاش که عصای خود را از من بردارد، و هیبت او مرا نترساند. ۳۴ 34
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
آنگاه سخن می‌گفتم و از او نمی ترسیدم، لیکن من در خودچنین نیستم. ۳۵ 35
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< ایّوب 9 >