< ایّوب 37 >

«از این نیز دل می‌لرزد و از جای خودمتحرک می‌گردد. ۱ 1
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
گوش داده، صدای آواز او را بشنوید، و زمزمه‌ای را که از دهان وی صادر می‌شود، ۲ 2
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
آن را در زیر تمامی آسمانهامی فرستد، و برق خویش را تا کرانهای زمین. ۳ 3
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
بعد از آن صدای غرش می‌کند و به آواز جلال خویش رعد می‌دهد و چون آوازش شنیده شدآنها را تاخیر نمی نماید. ۴ 4
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
خدا از آواز خودرعدهای عجیب می‌دهد. اعمال عظیمی که ماآنها را ادراک نمی کنیم به عمل می‌آورد، ۵ 5
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
زیرابرف را می‌گوید: بر زمین بیفت. و همچنین بارش باران را و بارش بارانهای زورآور خویش را. ۶ 6
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
دست هر انسان را مختوم می‌سازد تا جمیع مردمان اعمال او را بدانند. ۷ 7
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
آنگاه وحوش به ماوای خود می‌روند و در بیشه های خویش آرام می‌گیرند. ۸ 8
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
از برجهای جنوب گردباد می‌آید و ازبرجهای شمال برودت. ۹ 9
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
از نفخه خدا یخ بسته می‌شود و سطح آبها منجمد می‌گردد. ۱۰ 10
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
ابرها رانیز به رطوبت سنگین می‌سازد و سحاب، برق خود را پراکنده می‌کند. ۱۱ 11
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
و آنها به دلالت او به هر سو منقلب می‌شوند تا هرآنچه به آنها امرفرماید بر روی تمامی ربع مسکون به عمل آورند. ۱۲ 12
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
خواه آنها را برای تادیب بفرستد یا به جهت زمین خود یا برای رحمت. ۱۳ 13
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
«ای ایوب این را استماع نما. بایست و دراعمال عجیب خدا تامل کن. ۱۴ 14
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
آیا مطلع هستی وقتی که خدا عزم خود را به آنها قرار می‌دهد وبرق، ابرهای خود را درخشان می‌سازد؟ ۱۵ 15
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
آیا تواز موازنه ابرها مطلع هستی؟ یا از اعمال عجیبه اوکه در علم، کامل است. ۱۶ 16
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
که چگونه رختهای توگرم می‌شود هنگامی که زمین از باد جنوبی ساکن می‌گردد. ۱۷ 17
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
آیا مثل او می‌توانی فلک رابگسترانی که مانند آینه ریخته شده مستحکم است؟ ۱۸ 18
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
ما را تعلیم بده که با وی چه توانیم گفت، زیرا به‌سبب تاریکی سخن نیکو نتوانیم آورد. ۱۹ 19
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
آیا چون سخن گویم به او خبر داده می‌شود یاانسان سخن گوید تا هلاک گردد. ۲۰ 20
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
و حال آفتاب را نمی توان دید هرچند در سپهر درخشان باشد تاباد وزیده آن را پاک کند. ۲۱ 21
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
درخشندگی طلایی از شمال می‌آید و نزد خدا جلال مهیب است. ۲۲ 22
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
قادر مطلق را ادراک نمی توانیم کرد، او در قوت وراستی عظیم است و در عدالت کبیر که بی‌انصافی نخواهد کرد. ۲۳ 23
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
لهذا مردمان از او می‌ترسند، امااو بر جمیع دانادلان نمی نگرد.» ۲۴ 24
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< ایّوب 37 >