< ایّوب 31 >

«با چشمان خود عهد بسته‌ام، پس چگونه بر دوشیزه‌ای نظر افکنم؟ ۱ 1
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
زیراقسمت خدا از اعلی چیست؟ و نصیب قادرمطلق، از اعلی علیین؟ ۲ 2
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
آیا آن برای شریران هلاکت نیست؟ و به جهت عاملان بدی مصیبت نی؟ ۳ 3
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
آیا او راههای مرا نمی بیند؟ و جمیع قدمهایم را نمی شمارد؟ ۴ 4
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
اگر با دروغ راه می‌رفتم یا پایهایم با فریب می‌شتابید، ۵ 5
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
مرا به میزان عدالت بسنجد، تا خدا کاملیت مرا بداند. ۶ 6
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
اگرقدمهایم از طریق آواره گردیده، و قلبم در‌پی چشمانم رفته، و لکه‌ای به‌دستهایم چسبیده باشد، ۷ 7
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
پس من کشت کنم و دیگری بخورد، ومحصول من از ریشه‌کنده شود. ۸ 8
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
اگر قلبم به زنی فریفته شده، یا نزد در همسایه خود در کمین نشسته باشم، ۹ 9
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
پس زن من برای شخصی دیگرآسیا کند، و دیگران بر او خم شوند. ۱۰ 10
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
زیرا که آن قباحت می‌بود و تقصیری سزاوار حکم داوران. ۱۱ 11
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
چونکه این آتشی می‌بود که تا ابدون می‌سوزانید، و تمامی محصول مرا از ریشه می‌کند. ۱۲ 12
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
اگر دعوی بنده و کنیز خود را ردمی کردم، هنگامی که بر من مدعی می‌شدند. ۱۳ 13
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
پس چون خدا به ضد من برخیزد چه خواهم کرد؟ و هنگامی که تفتیش نماید به او چه جواب خواهم داد؟ ۱۴ 14
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
آیا آن کس که مرا در رحم آفریداو را نیز نیافرید؟ و آیا کس واحد، ما را در رحم نسرشت؟ ۱۵ 15
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
«اگر مراد مسکینان را از ایشان منع نموده باشم، و چشمان بیوه‌زنان را تار گردانیده، ۱۶ 16
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
اگرلقمه خود را به تنهایی خورده باشم، و یتیم از آن تناول ننموده، ۱۷ 17
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
و حال آنکه او از جوانیم با من مثل پدر پرورش می‌یافت، و از بطن مادرم بیوه‌زن را رهبری می‌نمودم. ۱۸ 18
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
اگر کسی را از برهنگی هلاک دیده باشم، و مسکین را بدون پوشش، ۱۹ 19
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
اگر کمرهای او مرا برکت نداده باشد، و از پشم گوسفندان من گرم نشده، ۲۰ 20
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
اگر دست خود را بر یتیم بلند کرده باشم، هنگامی که اعانت خود را دردروازه می‌دیدم، ۲۱ 21
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
پس بازوی من از کتفم بیفتد، و ساعدم از قلم آن شکسته شود. ۲۲ 22
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
زیرا که هلاکت از خدا برای من ترس می‌بود و به‌سبب کبریایی او توانایی نداشتم. ۲۳ 23
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
اگر طلا را امیدخود می‌ساختم و به زر خالص می‌گفتم تو اعتمادمن هستی، ۲۴ 24
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
اگر از فراوانی دولت خویش شادی می‌نمودم، و از اینکه دست من بسیار کسب نموده بود، ۲۵ 25
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
اگر چون آفتاب می‌تابید بر آن نظرمی کردم و بر ماه، هنگامی که با درخشندگی سیرمی کرد. ۲۶ 26
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
و دل من خفیه فریفته می‌شد و دهانم دستم را می‌بوسید. ۲۷ 27
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
این نیز گناهی مستوجب قصاص می‌بود زیرا خدای متعال را منکرمی شدم. ۲۸ 28
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
اگر از مصیبت دشمن خود شادی می‌کردم یا حینی که بلا به او عارض می‌شد وجدمی نمودم، ۲۹ 29
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
و حال آنکه زبان خود را از گناه ورزیدن بازداشته، بر جان او لعنت را سوال ننمودم. ۳۰ 30
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
اگر اهل خیمه من نمی گفتند: کیست که از گوشت او سیر نشده باشد، ۳۱ 31
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
غریب درکوچه شب را به‌سر نمی برد و در خود را به روی مسافر می‌گشودم. ۳۲ 32
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
اگر مثل آدم، تقصیر خود رامی پوشانیدم و عصیان خویش را در سینه خودمخفی می‌ساختم، ۳۳ 33
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
از این جهت که از انبوه کثیرمی ترسیدم و اهانت قبایل مرا هراسان می‌ساخت، پس ساکت مانده، از در خود بیرون نمی رفتم. ۳۴ 34
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
کاش کسی بود که مرا می‌شنید، اینک امضای من حاضر است. پس قادر مطلق مرا جواب دهد. و اینک کتابتی که مدعی من نوشته است. ۳۵ 35
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
یقین که آن را بر دوش خود برمی داشتم و مثل تاج برخود می‌بستم. ۳۶ 36
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
شماره قدمهای خود را برای اوبیان می‌کردم و مثل امیری به او تقرب می‌جستم. ۳۷ 37
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
اگر زمین من بر من فریاد می‌کرد و مرزهایش با هم گریه می‌کردند، ۳۸ 38
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
اگر محصولاتش را بدون قیمت می‌خوردم و جان مالکانش را تلف می‌نمودم، ۳۹ 39
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
پس خارها به عوض گندم وکرکاس به عوض جو بروید.» سخنان ایوب تمام شد. ۴۰ 40
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< ایّوب 31 >